• Gida
  • Labarai da Rahotanni
    • Labarai
    • Rahotonni
    • Tattaunawa
  • Sharhi da Tsokaci
    • Sharhin Fim
    • Tsokaci
  • Masu Haskawa
    • Taurarin Fim
    • Marubuta
    • Mawaƙa
  • Addini da Rayuwa
    • Rayuwa
    • Iyalai
    • Al’adu
    • Addini
  • Ranar Murna
Tuesday, August 25, 2026
  • Login
Kannywood - News, reviews and more  › hausa
  • Gida
  • Labarai da Rahotanni
    • Labarai
    • Rahotonni
    • Tattaunawa
  • Sharhi da Tsokaci
    • Sharhin Fim
    • Tsokaci
  • Masu Haskawa
    • Taurarin Fim
    • Marubuta
    • Mawaƙa
  • Addini da Rayuwa
    • Rayuwa
    • Iyalai
    • Al’adu
    • Addini
  • Ranar Murna
No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai da Rahotanni
    • Labarai
    • Rahotonni
    • Tattaunawa
  • Sharhi da Tsokaci
    • Sharhin Fim
    • Tsokaci
  • Masu Haskawa
    • Taurarin Fim
    • Marubuta
    • Mawaƙa
  • Addini da Rayuwa
    • Rayuwa
    • Iyalai
    • Al’adu
    • Addini
  • Ranar Murna
No Result
View All Result
Kannywood - News, reviews and more  › hausa
No Result
View All Result
  • Gida
  • Labari
  • Addini
  • Al’adu
  • Iyali
  • Marubuta
  • Mawaƙa
  • Nijeriya
  • Ranar Murna
  • Rayuwa
  • Sharhin Fim
  • Tattaunawa
  • Taurari
  • Tsokaci

An ƙaddamar da gagarumin shirin sake fasalin ƙungiyar AFMAN

by ABBA MUHAMMAD
June 11, 2026
in Labarai
0
Halin da ‘yan fim ke ciki: Kannywood tana neman taimakon gaggawa – AFMAN 

Alhaji Salisu Mohammed Officer, Shugaban AFMAN na Ƙasa

0
SHARES
0
VIEWS
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsappShare on Telegram

ƘUNGIYAR Masu Shirya Finafinai ta Arewacin Nijeriya (AFMAN) ta fara aiwatar da wani gagarumin shirin sake wa kan ta fasali.

Shirin ya haɗa da sake tsara tsarin shugabanci a matakin ƙasa da jihohi, tare da tsawaita wa’adin shugabannin riƙon ƙwarya da shekara guda domin tabbatar da ci gaba da aiwatar da sauye-sauyen da ake buƙata.

An cimma wannan matsaya ne a taron Kwamitin Zartarwa na Ƙasa (NEC) na ƙungiyar wanda aka gudanar ranar Talata, 9 ga Yuni, 2026, a hedikwatar AFMAN da ke Zoo Road a Kano.

Taron, wanda ya samu halartar manyan shugabannin ƙungiyar ƙarƙashin jagorancin Shugaban AFMAN na Ƙasa, Alhaji Salisu Mohammed Officer, ya mayar da hankali ne kan hanyoyin sake gina ƙungiyar domin ta dace da buƙatun zamani da kuma cigaban masana’antar Kannywood.

A jawabin sa na buɗe taron, Alhaji Officer ya jaddada muhimmancin haɗin kai da kuma aiwatar da gyare-gyaren da za su mayar da AFMAN ƙungiya mai ƙarfi, tasiri da amfani ga membobin ta da al’umma baki ɗaya.

Bayan tattaunawa mai zurfi, kwamitin ya amince da gudanar da cikakken nazari kan tsarin ƙungiyar, manufofin ta da hanyoyin gudanar da ayyukan ta, da nufin samar da sabuwar AFMAN da za ta iya fuskantar ƙalubalen da masana’antar shirya finafinai ke fuskanta a wannan zamani.

Daga cikin manyan ƙudirorin da aka amince da su akwai tsawaita wa’adin shugabannin riƙon ƙwarya na ƙasa da shekara guda, har zuwa lokacin da za a kammala sabon tsarin shugabanci da ake shirin samarwa.

Haka kuma, kwamitin ya amince da cike gurabe shida da suka rage babu masu riƙe da su a cikin Kwamitin Zartarwa na Ƙasa, domin cika adadin shugabanni goma sha uku da kundin tsarin ƙungiyar ya tanada.

A wani mataki na sake fasalin shugabanci, an amince da sake duba da sake tsara shugabannin AFMAN a dukkan jihohin Arewa, tare da sabunta wa’adin kwamitocin riƙon ƙwarya na jihohi da shekara guda yayin da ake ci gaba da aiwatar da sauye-sauyen da aka tsara.

Domin tabbatar da ingantaccen aiki a matakin jihohi, kwamitin ya ɗora wa Sakatare Janar na AFMAN, Alhaji Sani Sule Katsina, da Sakataren Yaɗa Labarai, Malam Mahmood Mukhtar Daneji, alhakin tantance ayyukan shugabanni da sakatarorin jihohi tare da gabatar da shawarwari kan maye gurbin waɗanda ba su gudanar da ayyukan su yadda ya kamata ba.

Har ila yau, taron ya amince da samar da gajerun saƙonnin wayar da kai domin ilimantar da al’umma kan matsalolin da suka haɗa da rashin tsaro, shaye-shaye a tsakanin matasa, lalacewar tarbiyya da kuma rashin ɗa’a a harkokin siyasa.

Kwamitin ya yanke shawarar riƙa gudanar da taron Kwamitin Zartarwa na Ƙasa a ƙarshen kowane wata, ko dai ta hanyar taron zahiri ko na yanar gizo, domin tabbatar da ci gaba da bibiyar ayyuka da kuma aiwatar da shawarwarin da aka yanke.

Bugu da ƙari, an bai wa Shugaban Kwamitin Amintattu (BoT) na AFMAN, Malam Abdullahi Sani Abdullahi, alhakin sa ido da bayar da shawarwari kan yadda za a aiwatar da shirin sake fasali da sake tsara ƙungiyar har zuwa lokacin da za a kammala shi.

A ƙarshe, Kwamitin Zartarwar ya yi kira ga dukkan membobin AFMAN da su rungumi sulhu, haɗin kai da fahimtar juna domin cigaban ƙungiyar da kuma bunƙasar masana’antar shirya finafiinai ta Arewa.

An rufe taron cikin nasara, inda Shugaban Ƙungiyar ya yaba wa mahalarta bisa gudunmawar da suka bayar wajen samar da muhimman shawarwari da ake sa ran za su kawo sabon sauyi da cigaba a tafiyar AFMAN.

Loading

Previous Post

Hotuna: Taron taya Hadiza Kabara murnar tarewa a sabon gidan ta a Kano

Next Post

Za a gudanar da bikin baje-kolin finafinai na Kaduna na Kasa da Kasa karo na tara

Related Posts

Mutuwar aure na ƙaddara ce – Jaruma Khadija Yobe
Labarai

Mutuwar aure na ƙaddara ce – Jaruma Khadija Yobe

August 23, 2026
Aina’u Ade ta raba wa tsofaffin jaruman Kannywood tallafin kuɗi
Labarai

Aina’u Ade ta raba wa tsofaffin jaruman Kannywood tallafin kuɗi

August 23, 2026
Ƙungiyar ‘Triple R Kannywood’ ta ziyarci jarumi Tanimu Akawu a asibiti
Labarai

Ƙungiyar ‘Triple R Kannywood’ ta ziyarci jarumi Tanimu Akawu a asibiti

August 23, 2026
Ƙungiyar Triple R ta ba jarumin Kannywood Mustapha Musty tallafin N500,000
Labarai

Ƙungiyar Triple R ta ba jarumin Kannywood Mustapha Musty tallafin N500,000

August 18, 2026
Yadda na gamu da ibtila’in karaya a ƙafa – Jarumi Ɗan’azumi Kamaye
Labarai

Yadda na gamu da ibtila’in karaya a ƙafa – Jarumi Ɗan’azumi Kamaye

August 14, 2026
Tozali TV zai yi bikin Henna Ball da karrama masu ƙwazo da tallafa wa waɗanda suka tsira daga hare-hare a ranar 31 ga Oktoba
Labarai

Tozali TV zai yi bikin Henna Ball da karrama masu ƙwazo da tallafa wa waɗanda suka tsira daga hare-hare a ranar 31 ga Oktoba

August 8, 2026
Next Post
Za a gudanar da bikin baje-kolin finafinai na Kaduna na Kasa da Kasa karo na tara

Za a gudanar da bikin baje-kolin finafinai na Kaduna na Kasa da Kasa karo na tara

  • Home
  • Game Da Mu
  • Privacy Policy
  • Contact Us

© 2024 Mujallar Fim

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labari
  • Addini
  • Al’adu
  • Iyali
  • Marubuta
  • Mawaƙa
  • Nijeriya
  • Ranar Murna
  • Rayuwa
  • Sharhin Fim
  • Tattaunawa
  • Taurari
  • Tsokaci

© 2024 Mujallar Fim

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In
error: Content is protected !!