HUKUMAR Tace Finafinai ta Jihar Kano ta ƙaryata ji-ta- ji-tar cewa wai ta janye dakatarwar da ta ƙaƙaba wa wasu fitattun jaruman Kannywood biyu, Adam Garba da Amina Uba Hassan.
A cikin ‘yan kwanakin nan, wasu rahotanni sun bazu a soshiyal midiya suna iƙirarin cewa an gudanar da wata ganawa tsakanin hukumar da jaruman, inda aka cimma matsayar janye dakatarwar da aka yi musu.
Idan kun tuna, tun a ranar 16 ga Mayu ne hukumar ta ba da sanarwar dakatar da jaruman biyu daga duk wata harkar fim a jihar har tsawon shekara guda, bisa rawar da suka taka a wani bidiyo da hukumar ta bayyana a matsayin wanda ya saɓa wa tarbiyya da kyawawan ɗabi’u.
Hukumar ta bayyana cewa matakin ya kasance wani ɓangare na ƙoƙarin ta na tabbatar da tsaftace harkar shirya finafinai da kuma tabbatar da bin dokoki da ƙa’idojin da ta shimfiɗa domin kare martabar al’umma da al’adun jihar.
Dakatarwar tana nufin an haramta wa Adam da Amina shiga ko gudanar da duk wani aiki da ya shafi shirya finafinai a Jihar Kano na tsawon shekara guda.
Haka kuma, dokar da ta kafa hukumar ta ba ta ikon ɗaukar irin wannan mataki kan duk wanda ya karya ƙa’idojin ta, tare da tanadin hukunci mai tsauri ga masu bijirewa.
Binciken da mujallar Fim ta gudanar ya nuna cewa rahotannin da ake yaɗawa na cewa an janye dakatarwar ba su da tushe, kuma hukumar ba ta fitar da wata sanarwa da ke tabbatar da hakan ba.
Da yake magana da mujallar Fim, Babban Sakataren Hukumar Tace Finafinai ta Jihar Kano, Alhaji Abba El-Mustapha, ya musanta rahotannin, yana mai cewa: “Ba mu san da irin wannan labari ba. Idan akwai wani muhimmin bayani daga hukumar, za a ji shi ne daga bakin Jami’in Yaɗa Labaran Hukumar, domin shi ne ke da ikon sanar da duk wani matsayi ko sanarwa a hukumance.”

A cewar sa, har zuwa yanzu, dakatarwar da aka yi wa jaruman biyu tana nan daram, kuma babu wani sauyi da aka samu a kan matakin da hukumar ta ɗauka.
![]()







