Kwamitin shirya taron Ranar Marubutan Hausa ta Duniya na bana ya ce za a rufe rajistar halarta taron saboda an riga an kai adadin mutanen da ake buƙata domin gudanar da taron cikin tsari da aminci.
A game da hakan ne kwamitin ya tsaida ranar Alhamis mai zuwa a matsayin rana ta ƙarshe ta kammala rajista.
Sakataren Kwamitin Shirya Taron, Dakta Abdulrahman Aliyu, shi ne ya bayyana haka a cikin wata sanarwa da raba wa manema labarai a yau
Ya ce daga wannan ranar babu wanda zai ƙara iya yin rajista ko canza bayanan rajistar sa da aka riga aka kammala.
Aliyu ya ce wannan matakin ya zama dole ne saboda kwamitin ya fara shirin samar da ingantattun abubuwan more rayuwa da jin daɗin mahalarta taron, domin tabbatar da cewa taron zai gudana bisa tsarin da ake gudanar da taruka na ƙasa da ƙasa.
Haka kuma ya ce kwamitin ya tanadi wurin kwana mai inganci ga dukkan mahalarta da suka yi rajista a kan lokaci; abinci da sha mai kyau da tsafta, da kuma tsarin taro na zamani da zai bai wa kowa damar koyo da musayar ra’ayi da hulɗa da ƙwararru daga sassa daban-daban na duniya.
Ya ci gaba da cewa. “Taron Ranar Marubuta Hausa na Duniya, 2025, wanda za a gudanar a Jihar Jigawa, na da nufin ɗaga martabar harshen Hausa da marubuta, tare da haɗa su da sabbin fasahohi da dabarun da ake amfani da su a duniya wajen rubutu, fassara, da ilimin harshe.”
Kwamitin yana yaba wa duk wanda ya nuna sha’awa ko ya riga ya yi rajista, tare da neman afuwar waɗanda ba su samu damar kammala rajista ba.
A cewar sa, wanda ke sha’awar zuwa taron bai yi rajista ba zai iya halarta, amma ba za a ba shi masauki da kayan da suka shafi taron ba.
![]()







