Kwamitin Zartarwa na Ƙasa na ƙungiyar Tinubu/Uba Sani Mobilisation Network ya naɗa fitaccen mawaƙin siyasa kuma mazaunin Kaduna, Jamilu Sa’idu (Ɗan Masu Kuɗi), a matsayin Shugaban Sashen Nishaɗantarwa na Midiya (Head of Media Entertainment) na ƙungiyar.
Mujallar Fim ta ruwaito cewa naɗin yana da nasaba da yaƙin neman babban zaɓen shekarar 2027 da za a yi a Nijeriya.
A cikin takardar naɗin da ke ɗauke da kwanan watan 8 ga Mayu, 2026, ƙungiyar ta bayyana cewa an zaɓi Jamilu ne bisa la’akari da ƙwarewar sa a fannin sadarwar zamani, ƙirƙire-ƙirƙire, da kuma jajircewar sa wajen yaɗa manufofin shirin Renewed Hope Agenda na Shugaban Ƙasa Bola Ahmed Tinubu tare da tallata nasarorin gwamnatin Gwamna Uba Sani.
Takardar ta ƙara da cewa naɗin zai fara aiki nan take, inda aka umurci sabon shugaban sashen da ya riƙa karɓar umurni da shawarwari daga jagoran harkokin jihohi na ƙungiyar domin tabbatar da nasarar ayyukan sa.
A matsayin sa na shugaban sashen nishaɗantarwa a ɓangaren midiya, Jamilu zai jagoranci amfani da masana’antar nishaɗi wajen wayar da kan jama’a kan manufofi da shirye-shiryen ƙungiyar.
Haka kuma, zai taimaka wajen tattara magoya baya ta hanyar nishaɗi, yaƙi da yaɗuwar bayanan ƙarya, da kuma haskaka nasarorin gwamnatocin jam’iyyar APC a matakan tarayya da jihohi.
Bugu da ƙari, ƙungiyar ta buƙaci sabon shugaban sashen da ya miƙa takardar amincewar sa da wannan naɗi ga Sakatare Janar na ƙungiyar cikin mako guda bayan karɓar takardar naɗin.
Da yake taya shi murna, jagoran Kwamitin Zartarwa na Ƙasa na ƙungiyar, Dakta Abdulmumini Aminu Zaria, ya bayyana fatan cewa Jamilu Ɗan Masu Kuɗi zai yi amfani da gogewar sa da tasirin sa a fagen nishaɗi wajen ƙara ƙarfafa manufofi da ayyukan ƙungiyar, tare da yi masa fatan alheri a sabon muƙamin da aka ɗora masa.
![]()







