A YAU Juma’a, 18 ga Yuni, 2021 aka ɗaura auren fittacciyar tsohuwar jaruma Naja’atu Muhammad, wadda aka fi sani da Murjanatu ‘Yarbaba, da fitaccen ɗan ƙwallon Nijeriya ɗin nan Abdullahi Shehu.
An ɗaura auren da misalin ƙarfe 1:15 na rana, bayan an idar da sallar Juma’a a babban masallacin Juma’a na Umar Bin Khattab da ke Titin Zariya, Kano, a kan sadaki N50,000.
Manyan mutane da wakilan gwamnan Jihar Sokoto sun wakilci ɗaurin auren, a ciki har da babban aminin angon kuma abokin sana’ar sa, Ahmed Musa.

Wata majiya ta shaida wa mujallar Fim cewa babu wani shagalin biki da za a yi yanzu, saboda rasa mahaifiyar da amaryar ta yi a ranar Laraba, 16 ga wannan wata, wato shekaranjiya kenan.
Allah ya jiƙan ta da rahama, su kuma sababbin ma’auratan Allah ya ba su zaman lafiya da zuri’a ɗayyiba.

![]()







