• Gida
  • Labarai da Rahotanni
    • Labarai
    • Rahotonni
    • Tattaunawa
  • Sharhi da Tsokaci
    • Sharhin Fim
    • Tsokaci
  • Masu Haskawa
    • Taurarin Fim
    • Marubuta
    • Mawaƙa
  • Addini da Rayuwa
    • Rayuwa
    • Iyalai
    • Al’adu
    • Addini
  • Ranar Murna
Thursday, May 14, 2026
  • Login
Kannywood - News, reviews and more  › hausa
  • Gida
  • Labarai da Rahotanni
    • Labarai
    • Rahotonni
    • Tattaunawa
  • Sharhi da Tsokaci
    • Sharhin Fim
    • Tsokaci
  • Masu Haskawa
    • Taurarin Fim
    • Marubuta
    • Mawaƙa
  • Addini da Rayuwa
    • Rayuwa
    • Iyalai
    • Al’adu
    • Addini
  • Ranar Murna
No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai da Rahotanni
    • Labarai
    • Rahotonni
    • Tattaunawa
  • Sharhi da Tsokaci
    • Sharhin Fim
    • Tsokaci
  • Masu Haskawa
    • Taurarin Fim
    • Marubuta
    • Mawaƙa
  • Addini da Rayuwa
    • Rayuwa
    • Iyalai
    • Al’adu
    • Addini
  • Ranar Murna
No Result
View All Result
Kannywood - News, reviews and more  › hausa
No Result
View All Result
  • Gida
  • Labari
  • Addini
  • Al’adu
  • Iyali
  • Marubuta
  • Mawaƙa
  • Nijeriya
  • Ranar Murna
  • Rayuwa
  • Sharhin Fim
  • Tattaunawa
  • Taurari
  • Tsokaci

Zargin yaɗa baɗala: Kotu ta yanke wa Sayyada Sadiya Haruna hukunci

by DAGA MUHAMMAD LAWAN RANO
August 23, 2021
in Labarai
0
Zargin yaɗa baɗala: Kotu ta yanke wa Sayyada Sadiya Haruna hukunci
0
SHARES
0
VIEWS
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsappShare on Telegram

WATA kotu a birnin Kano a yau ta yanke wa jaruma kuma furodusar finafinan Hausa, Sayyada Sadiya Haruna, hukuncin komawa Islamiyya.

Sadiya dai ta shahara wajen sayar da kayan ƙarin ni’ima da na ƙarfin maza ta hanyar soshiyal midiya, kuma tsarin yin tallar ta ya na ba wasu mutanen mamaki ko haushi, wanda hakan ne ya sa jami’an Hukumar Hisba su ka kama ta a ranar Juma’a da ta gabata, 20 ga Agusta, 2021.

Hukumar ta damƙa ta ga hannun rundunar ‘yan sanda ta Jihar ta Kano, su kuma ‘yan sandan su ka maka ta a kotun shari’ar Musulunci da ke Hukumar Hisbah ta Jihar Kano bisa zargin yaɗa hotunan batsa a kafafen sada zumunta da sunan sana’a.

‘Yan sandan sun gurfanar da kyakkyawar jarumar ne a gaban Mai Shari’a Ali Jibril Ɗanzaki, wanda shi kuma bayan an gabatar masa da bayanai sai ya yanke mata hukuncin sanya ta a makarantar Islamiyya mai suna Darul Hadith har na tsawon wata bakwai.

Ɗaya daga sharuɗɗan da alƙalin ya gindaya mata shi ne za ta riƙa zuwa makarantar tare da rakiyar jami’an Hukumar Hisba.

Haka kuma ya bayyana cewa a duk sa’ilin da ta je makarantar, za ta riƙa sa hannu a wata takarda, shaidar ta je ɗin.

Daga nan aka sake ta, ta tafi gida.

Wakilin mujallar Fim ya so jin ta bakin jarumar kan wannan hukunci da aka yanke mata, amma abin ya faskara.

Kotu ta umarci Sayyada Sadiya Haruna ta koma Islamiyya

Ita dai Sayyada Sadiya Haruna, da yawa su na mata kallon ‘yar taratsi, wadda ke amfani da kalaman batsa da rawar kai a bidiyoyin tallar kayan gyaran jiki da na ƙarin ni’ima da ƙarfin maza. Haka kuma ta kan yawan ambaton ƙirar jikin ta da kyan fuskar ta.

To amma kuma ta kan shirya bidiyoyin waƙoƙin yabon Manzo Allah (s.a.w.), inda ake nuno ta ta na bin waƙoƙin bege da wasu su ka rera.

Ta raɗa wa kan ta laƙabin Sayyada domin nuna shauƙin ta game da son Manzon Allah (s.a.w.).

Kama ta da ‘yan Hisba su ka yi ya jawo ka-ce-na ce a soshiyal midiya, inda wasu ke cewa an kyauta, ya kamata a ɗaure ta, to amma wasu kuma na cewa sam ba daidai ba ne.

Jaruma Ummah Shehu na daga cikin masu kare Sadiya, ta na faɗin cewa kama ta da aka yi an keta mata mutunci kuma Allah ya ce ba a shiga tsakanin sa da bawan sa. 

Wasu masu maganar sun yi wa Umma Shehu caa, su na cewa sam ba ta nuna kishin Musulunci ba kuma kama Sadiya abu ne da ya dace.

Loading

Tags: hausa filmsHukimar HisbahKannywoodMai Shari'a Ali Jibril JanzakiSayyada Sadiya HarunaUmmah Shehu
Previous Post

Ban yi soyayya da Ummi Rahab ba – Adam A. Zango

Next Post

Hisbah ta Kano ta shiga farautar Ummah Shehu

Related Posts

Rasuwar dattijon Kannywood, Nura Shareef, ta girgiza ‘yan fim
Labarai

Rasuwar dattijon Kannywood, Nura Shareef, ta girgiza ‘yan fim

February 22, 2026
Daraktar fim ta ƙi karɓar awad saboda kisan gillar da Isra’ila take yi a Gaza
Labarai

Daraktar fim ta ƙi karɓar awad saboda kisan gillar da Isra’ila take yi a Gaza

February 21, 2026
Fitaccen furodusa Kunle Afolayan ya yi haɗin gwiwa da Jamhuriyar Benin kan shirya finafinai
Labarai

Fitaccen furodusa Kunle Afolayan ya yi haɗin gwiwa da Jamhuriyar Benin kan shirya finafinai

February 19, 2026
An naɗa Farfesa Tengya matsayin sabon shugaban Cibiyar Koyon Finafinai ta Ƙasa
Labarai

An naɗa Farfesa Tengya matsayin sabon shugaban Cibiyar Koyon Finafinai ta Ƙasa

February 15, 2026
Alƙali ya ci Samha Inuwa tara ko ta je kurkuku wata 6
Labarai

Alƙali ya ci Samha Inuwa tara ko ta je kurkuku wata 6

February 13, 2026
Hukumar EFCC ta kama jarumar Kannywood, Samha Inuwa, saboda goge majina da takardun naira
Labarai

Hukumar EFCC ta kama jarumar Kannywood, Samha Inuwa, saboda goge majina da takardun naira

February 3, 2026
Next Post
Hisbah ta Kano ta shiga farautar Ummah Shehu

Hisbah ta Kano ta shiga farautar Ummah Shehu

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

  • Home
  • Game Da Mu
  • Privacy Policy
  • Contact Us

© 2024 Mujallar Fim

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labari
  • Addini
  • Al’adu
  • Iyali
  • Marubuta
  • Mawaƙa
  • Nijeriya
  • Ranar Murna
  • Rayuwa
  • Sharhin Fim
  • Tattaunawa
  • Taurari
  • Tsokaci

© 2024 Mujallar Fim

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In
error: Content is protected !!