INNA lillahi wa inna ilaihir raji’un! Allah ya yi wa fitaccen jarumi kuma marubucin labaran finafinai, Alhaji Yusuf Barau rasuwa.
Yusuf Barau, wanda tsohon ma’aikaci ne a Hukumar Wasanni, Al’adu da Yawon Shaƙatawa ta Jihar Kaduna, ya rasu a yau a asibitin Isolation Centre da ke Down Quarters, Kakuri, Kaduna.
Marigayin ya rasu ya na da kimanin shekara 61 a duniya.
Haka kuma ya rasu ya bar ‘ya’ya takwas da mata ɗaya.

Aminin sa, fitaccen ɗan wasan ban Malam Musa Mohammed Abdullahi, ya shaida wa mujallar Fim cewa shi marigayin da kan sa ne ya kai kan sa asibitin.
Za a yi jana’izar sa bayan sallar Isha’i a gidan su da ke garin su, Zariya, inda wan sa ya ce a kai gawar a rufe shi a can.
Haƙiƙa rasuwar Alhaji Yusuf Barau ta kaɗa hankalin ‘yan Kannywood, musamman abokan aikin sa, wato waɗanda su ka yi aiki da shi a industiri ko a Hukumar Wasanni, Al’adu da Yawon Shaƙatawa. Duk jikin jama’a ya yi sanyi. Kowa ya na ta yi masa addu’ar samun rahama.
Allah ya jiƙan sa da rahama. Ya kuma albarkaci dukkan abin da ya bari, amin.
Copyright © Fim Magazine. All rights reserved.
www.fimmagazine.com
![]()







