• Gida
  • Labarai da Rahotanni
    • Labarai
    • Rahotonni
    • Tattaunawa
  • Sharhi da Tsokaci
    • Sharhin Fim
    • Tsokaci
  • Masu Haskawa
    • Taurarin Fim
    • Marubuta
    • Mawaƙa
  • Addini da Rayuwa
    • Rayuwa
    • Iyalai
    • Al’adu
    • Addini
  • Ranar Murna
Thursday, August 13, 2026
  • Login
Kannywood - News, reviews and more  › hausa
  • Gida
  • Labarai da Rahotanni
    • Labarai
    • Rahotonni
    • Tattaunawa
  • Sharhi da Tsokaci
    • Sharhin Fim
    • Tsokaci
  • Masu Haskawa
    • Taurarin Fim
    • Marubuta
    • Mawaƙa
  • Addini da Rayuwa
    • Rayuwa
    • Iyalai
    • Al’adu
    • Addini
  • Ranar Murna
No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai da Rahotanni
    • Labarai
    • Rahotonni
    • Tattaunawa
  • Sharhi da Tsokaci
    • Sharhin Fim
    • Tsokaci
  • Masu Haskawa
    • Taurarin Fim
    • Marubuta
    • Mawaƙa
  • Addini da Rayuwa
    • Rayuwa
    • Iyalai
    • Al’adu
    • Addini
  • Ranar Murna
No Result
View All Result
Kannywood - News, reviews and more  › hausa
No Result
View All Result
  • Gida
  • Labari
  • Addini
  • Al’adu
  • Iyali
  • Marubuta
  • Mawaƙa
  • Nijeriya
  • Ranar Murna
  • Rayuwa
  • Sharhin Fim
  • Tattaunawa
  • Taurari
  • Tsokaci

Cewar Rarara: Zan tsaya takarar Majalisar Tarayya a 2023

by DAGA EL-ZAHARADEEN UMAR
October 25, 2021
in Labarai
0
Alhaji Dauda Adamu Kahutu (Rarara)

Alhaji Dauda Adamu Kahutu (Rarara)

0
SHARES
0
VIEWS
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsappShare on Telegram

SHAHARARREN mawaƙin nan kuma ɗan siyasa, Alhaji Dauda Adamu Kahutu (Rarara), ya bayyana cewa lallai maganar da ake yawo da ita ta batun tsayawar sa takarar zama ɗan Majalisar Wakilai ta Tarayya mai wakiltar Ƙananan Hukumomin Bakori da Ɗanja da ke Jihar Katsina gaskiya ce.

Rarara da kan sa ya  tabbatar wa da mujallar Fim haka a Katsina a wata zantawar da ta yi da shi a kan wasu batutuwa da su ka shafi waƙoƙin sa, musamman waƙar da ya ce talakawa ne su ka biya kuɗin yin ta da kuma batun tsayawar sa takara.

Ya ƙara da cewa ya zuwa yanzu akwai batun sabuwar waƙar da ya yi wadda talakawa su ka biya kuɗi domin bayyana ayyukan Shugaban Ƙasa Muhammadu Buhari.

Ya ce kwanan nan zai tsunduma zagaya jihohin Nijeriya domin nuna irin ayyukan da ya gano Buhari ya yi.

Ya ce, “Idan Allah ya sa na kammala wannan aikin da ke gaba na, to zan tsaya takarar ɗan Majalisar Tarayya na Ƙananan Hukumomin Bakori da kuma Ɗanja. Idan kuma wannan aiki ya sha gaba na, sai kuma a duba batun nan gaba.”

A cewar Rarara, ya yi niyyar gano ayyukan Shugaban Ƙasa guda 90 amma sai ya gano 900,000 wanda ya ke ganin aikin ya na da yawa, amma dai idan ya samu damar kammala wannan aikin zai dawo kan batun yin takarar sa wanda tuni ya fara yawo a gidajen siyasa.

Rarara ya bayyana cewa zaɓen shugabannin siyasa da aka gudanar a makon jiya a Katsina ya yi masa kyau, kuma ya yi yadda ake so, saboda haka ya na fatan wannan zaɓen zai taimaka wajen ƙara samun nasarar jam’iyyar su ta APC a zaɓe mai zuwa.

Bugu da ƙari, mawaƙin ya yaba da irin tsarin da aka bi wajen samar da shuwagabannin, ya ce abin ya yi matuƙar burge shi, kuma a Nijeriya babu inda aka yi abin da ya dace kamar Jihar Katsina.

Ya ce hatta Shugaban Ƙasa ya yaba da ƙoƙarin Gwamna Aminu Bello Masari a kan haka.

Rarara ya ce, “Idan ka duba da kyau, tun daga zaɓen shuwagabanni na matakin rumfuna da ƙananan hukumomi da na jiha babu wanda ya ce bai yarda da tsarin da aka bi ba, saboda haka wannan shi ne ake kira shugabanci. 

“Masari ya yi matuƙar ƙoƙari wajen haɗa kan ‘yan jam’iyyar APC a Jihar Katsina.”

Loading

Tags: Aminu Bello MasariAPCBakoriDanjaDauda Kahutu RararaHouse of RepresentativesMajalisar Wakilai ta Tarayyamawakan hausaShugaba Muhammadu Buharisiyasatakarazabe
Previous Post

Zuwa ga Adam A. Zango: Ina aka kwana da marayun ka na Zariya?

Next Post

‘Yan sanda na binciken yadda jarumi ya harbe mai shirya fim da bindiga a lokeshin

Related Posts

Tozali TV zai yi bikin Henna Ball da karrama masu ƙwazo da tallafa wa waɗanda suka tsira daga hare-hare a ranar 31 ga Oktoba
Labarai

Tozali TV zai yi bikin Henna Ball da karrama masu ƙwazo da tallafa wa waɗanda suka tsira daga hare-hare a ranar 31 ga Oktoba

August 8, 2026
Tsohuwar matar Adam Zango, Maimuna Musa, ta tabbatar da dalilin rabuwar auren su
Labarai

Tsohuwar matar Adam Zango, Maimuna Musa, ta tabbatar da dalilin rabuwar auren su

August 2, 2026
Fitaccen mawaƙin siyasa Muhammadu Buhari ‘Kosan Waka’ ya kwanta dama
Labarai

Fitaccen mawaƙin siyasa Muhammadu Buhari ‘Kosan Waka’ ya kwanta dama

August 2, 2026
Yadda gwajin ƙwayoyin halitta na jini ya kawo ƙarshen auren Adam A. Zango da Maimuna Musa bayan watanni 11
Labarai

Yadda gwajin ƙwayoyin halitta na jini ya kawo ƙarshen auren Adam A. Zango da Maimuna Musa bayan watanni 11

August 1, 2026
Jami’an gwamnati sun yi zama da Kannywood domin fara aiwatar da shirin ba da inshorar lafiya kyauta ga ‘yan fim na Kano
Labarai

Jami’an gwamnati sun yi zama da Kannywood domin fara aiwatar da shirin ba da inshorar lafiya kyauta ga ‘yan fim na Kano

July 15, 2026
Kannywood tana buƙatar farfaɗo da gidajen sinima domin bunƙasa tattalin arzikin ƙirƙira – Sani Mu’azu
Labarai

Kannywood tana buƙatar farfaɗo da gidajen sinima domin bunƙasa tattalin arzikin ƙirƙira – Sani Mu’azu

July 14, 2026
Next Post
Lokeshin ɗin shirya fim ɗin 'Rust' inda aka yi kisan

'Yan sanda na binciken yadda jarumi ya harbe mai shirya fim da bindiga a lokeshin

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

  • Home
  • Game Da Mu
  • Privacy Policy
  • Contact Us

© 2024 Mujallar Fim

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labari
  • Addini
  • Al’adu
  • Iyali
  • Marubuta
  • Mawaƙa
  • Nijeriya
  • Ranar Murna
  • Rayuwa
  • Sharhin Fim
  • Tattaunawa
  • Taurari
  • Tsokaci

© 2024 Mujallar Fim

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In
error: Content is protected !!