• Gida
  • Labarai da Rahotanni
    • Labarai
    • Rahotonni
    • Tattaunawa
  • Sharhi da Tsokaci
    • Sharhin Fim
    • Tsokaci
  • Masu Haskawa
    • Taurarin Fim
    • Marubuta
    • Mawaƙa
  • Addini da Rayuwa
    • Rayuwa
    • Iyalai
    • Al’adu
    • Addini
  • Ranar Murna
Sunday, August 23, 2026
  • Login
Kannywood - News, reviews and more  › hausa
  • Gida
  • Labarai da Rahotanni
    • Labarai
    • Rahotonni
    • Tattaunawa
  • Sharhi da Tsokaci
    • Sharhin Fim
    • Tsokaci
  • Masu Haskawa
    • Taurarin Fim
    • Marubuta
    • Mawaƙa
  • Addini da Rayuwa
    • Rayuwa
    • Iyalai
    • Al’adu
    • Addini
  • Ranar Murna
No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai da Rahotanni
    • Labarai
    • Rahotonni
    • Tattaunawa
  • Sharhi da Tsokaci
    • Sharhin Fim
    • Tsokaci
  • Masu Haskawa
    • Taurarin Fim
    • Marubuta
    • Mawaƙa
  • Addini da Rayuwa
    • Rayuwa
    • Iyalai
    • Al’adu
    • Addini
  • Ranar Murna
No Result
View All Result
Kannywood - News, reviews and more  › hausa
No Result
View All Result
  • Gida
  • Labari
  • Addini
  • Al’adu
  • Iyali
  • Marubuta
  • Mawaƙa
  • Nijeriya
  • Ranar Murna
  • Rayuwa
  • Sharhin Fim
  • Tattaunawa
  • Taurari
  • Tsokaci

Ummi Rahab za ta yi wuf! da Lilin Baba, har an biya sadaki an sa rana

by DAGA ALI KANO
May 24, 2022
in Ranar Murna
0
Amarya da ango, Lilin Baba da Ummi Rahab

Amarya da ango, Lilin Baba da Ummi Rahab

0
SHARES
0
VIEWS
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsappShare on Telegram

FITACCEN mawaƙi kuma jarumi a Kannywood, Shu’aibu Ahmed Abbas, wanda aka fi sani da Lilin Baba, ya biya sadakin fitacciyar jaruma Ummi Rahab, kuma har an sa masu rana.
 Tabbacin hakan ya fito ne daga Sulaiman Sir Zeesu, ɗaya daga cikin aminan Lilin Baba, a wani saƙo da ya wallafa a Instagram a daren jiya.

A saƙon, Sir Zeesu ya ƙara da cewa har an saka ranar bikin auren jarumar ta shirin ‘Wuff!’ da shi furodusa kuma jarumin shirin, tare da taya su murna.

Sai dai bai bayyana ranar bikin ba.

Ga abin da Sir Zeesu ya wallafa a shafin sa na Instagram:

Mun biya sadaki kuma an saka rana. Alhamdu lillahi ya Allah. It’s official. #SHURAN2022 Congratulations @lilin.baba @ummirahabofficial

Ɗan shekara 30 da haihuwa, shi dai Lilin Baba ɗan asalin Gwoza ne a Jihar Borno.

Ya shigo industiri a cikin 2016 a matsayin mawaƙi, inda ya fitar da waƙa mai taken ‘Arewa’.

Abin ya zo! Za su yi wuf! da juna

Kafin zuwan sa Kannywood, ya fara da tallar ƙanƙara ne (ice blocks) a bakin Bata, Kano, daga baya ya koma Abuja ya shiga sana’ar saida motoci.

Daga Abujan ne ya dawo Kaduna ya shiga harkar waƙa, kuma Allah ya yi masa nasibi a ciki.

A yanzu Lilin Baba ya na ɗaya daga cikin manyan mawaƙan Arewa, domin shi ne ma ya lashe gasar ‘Arewa Best R&B Music Act of the Year’ a bikin ‘City People Entertainment Awards’ na shekarar 2019.

Ya fara fitowa a fim ne a shirin ‘Hauwa Kulu’, yanzu kuma shi ne jarumin shirin nan mai dogon zango mai suna ‘Wuff!’ wanda ake nunawa a YouTube.

Labarin haɗewar sa da Ummi Rahab ba sabo ba ne, musamman bayan ya ƙwace ta daga hannun mawaƙi kuma jarumi Adam A. Zango, wanda ubangidan sa ne a da.

A lokacin rigimar jarumar da Zango, shi Zango ya zargi cewa wasu ne ke zuga ta har ta ke yo masa tsiwa, wanda a Kannywood an san da su Lilin Baba ya ke.

Ba da jimawa ba Lilin Baba da Ummi su ka bayyana soyayyar da ke tsakanin su da kuma niyyar su ta yin aure.

Yanzu ga abin zai tabbata. To, Allah ya sa alheri.

Loading

Tags: 'Wuff!'Adam A. ZangoArewa R&BaureCity People Entertainment AwardsGwozaKannywoodLilin BabamawakasadakiShu'aibu Ahmed AbbasSulaiman Sir ZeesuUmmi Rahab
Previous Post

Zan yi amfani da sarautar da aka ba ni wajen inganta rayuwar matasa, inji Fatima Lamaj

Next Post

Gwamnati za ta kashe naira miliyan 999 a kullum wajen ciyar da ‘yan makaranta miliyan 10

Related Posts

Uwargida na ce ta biya sadakin aure na da amarya ta – darakta Aminu Saira
Ranar Murna

Uwargida na ce ta biya sadakin aure na da amarya ta – darakta Aminu Saira

August 2, 2026
Bikin auren darakta Aminu Saira a Azare ya ja hankalin jama’a
Ranar Murna

Bikin auren darakta Aminu Saira a Azare ya ja hankalin jama’a

July 31, 2026
An taya Aisar, jikar marubuciya Sadiya Garba Yakasai, murnar cika shekaru 5
Ranar Murna

An taya Aisar, jikar marubuciya Sadiya Garba Yakasai, murnar cika shekaru 5

July 15, 2026
Jarumin Kannywood Tijjani Faraga ya aurar da ‘yar sa ta biyu
Ranar Murna

Jarumin Kannywood Tijjani Faraga ya aurar da ‘yar sa ta biyu

July 12, 2026
Mawaƙi Sa’eed Ja’afar ya samu ƙaruwa da ‘ya mace
Ranar Murna

Mawaƙi Sa’eed Ja’afar ya samu ƙaruwa da ‘ya mace

July 6, 2026
Furodusa Alhaji Sheshe da Khairiyyah sun zama ɗaya
Ranar Murna

Furodusa Alhaji Sheshe da Khairiyyah sun zama ɗaya

July 4, 2026
Next Post
Hajiya Sadiya Umar Farouq, Minista

Gwamnati za ta kashe naira miliyan 999 a kullum wajen ciyar da 'yan makaranta miliyan 10

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

  • Home
  • Game Da Mu
  • Privacy Policy
  • Contact Us

© 2024 Mujallar Fim

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labari
  • Addini
  • Al’adu
  • Iyali
  • Marubuta
  • Mawaƙa
  • Nijeriya
  • Ranar Murna
  • Rayuwa
  • Sharhin Fim
  • Tattaunawa
  • Taurari
  • Tsokaci

© 2024 Mujallar Fim

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In
error: Content is protected !!