BABBAN furodusa a Kannywood, Alhaji Abubakar Bashir Maishadda, ya bayyana cewa daga harkar fim ne ya samo kuɗin da ya buɗe katafaren shagon nan na sayar da tufafi da ya ƙaddamar a ranar Juma’a, don haka ba harka ce da zai yi wasa da ita ba.
Ya faɗa wa mujallar Fim cewa: “Harkar fim ita ce ni, ka ga kuwa in babu ita babu ni. Ko kuɗin da na buɗe shago, ai da fim na same su. Fim ba sana’ar da zan bari ba ne.”
An yi bikin buɗe shagon mai suna ‘Mai Shadda Textile’ a ranar Juma’a, 30 ga Satumba, 2022, wato shago mai lamba 5 da ke MYCA 7, Plaza, a Titin Gidan Zu, a Kano.
A yayin da ya ke tattaunawa da wakilin mu, Maishadda ya bayyana matuƙar farin ciki, ya ce: “Alhamdu lillah. Babu abin da zan ce wa Allah (s.w.t.) sai dai in gode masa. Na kuma yi farin ciki sosai da Allah ya nuna mani wannan lokaci.

“Kasancewar da ma irin wannan sana’ar mu na yin ta a ɓoye, wannan karon sai mu ka ga ya kamata mu bayyana shi saboda mutane su sani, saboda duk wani abu da ake nema na ɓangaren yaduddika, shaddodi, jakunkuna, takalma, duk mu na da su.
“Kuma in-sha Allahu za mu riƙa ba da farashi irin yadda ake ba da wa a kasuwa. Zai zamana da ka shiga cikin kasuwa ka haɗu da gosulo ran ka ya ɓaci, gwanda ka zo wurin mu ka saya.”
Dangane da yadda zai iya haɗa wannan kasuwancin da sana’ar fim kuwa, furodusan ya ce ai yayar sa da ƙanwar sa ne zai bar wa aikin gudanar da shagon yayin da shi kuma zai ci gaba da harkar sa ta fim.
Ya ce: “Ai wancan kasuwancin ba ni ne a kai ba, yaya ta ce da ƙanwa ta su ke kula da shagon.
“Harkar fim kuma harka ta ce da na ke kan yin ta. Harkar fim ita ce ni, ka ga kuwa in babu ita babu ni. Ko kuɗin da na buɗe shago, ai da fim na same su. Fim ba sana’ar da zan bari ba ne. Har gobe ina ci gaba da yi.”
Mawaƙin siyasa, Alhaji Dauda Adamu Abdullahi Kahutu (Rarara), shi ne uban taro a bikin ƙaddamarwar, wato shi ne ya jagoranci buɗe shagon.
Ɗimbin ‘yan fim da su ka halarci taron sun haɗa da Adam A. Zango, Daddy Hikima, Nura M. Inuwa, Yakubu Muhammad, El-Mu’az Birniwa, Umar Gombe, Rasheeda Adamu Abdullahi, Sadiq Zazzaɓi, Hafizu Bello, Aisha Ahmad Idris (Aishatulhumaira), da Abba Miko Yakasai, Mustapha Nabraska, Siddiqa J. Sarki, da sauran su.

Ita ma matar Maishadda, tsohuwar jaruma Hassana Muhammad, ta halarci taron tare da ‘yan’uwan su na jini.
Tun wajen ƙarfe 3:00 na rana aka fara taron, amma ba a tashi ba sai wajen ƙarfe 10:00 na dare saboda cincirindon mutane.



![]()








Comments 3