JARUMIN Kannywood, Alhaji Balarabe Jaji, ya yi bayani kan wasu hotuna da aka yaɗa a Facebook inda aka nuno kwance magashiyan a asibiti, da alamar ba ya da lafiya.
A cikin ‘yan kwanakin nan ne hotunan su ka ɓulla. A ciki, an ga Jaji ya na kwance a asibiti, idon sa ɗaya da bandeji.
Wasu da su ka ga hotunan sun yi tunanin a fim ne, yayin da wasu kuma ke tunanin da gaske shi ne aka yi wa aiki a ido.
Mujallar Fim ta amsa kiran mutane da dama masu tambayar gaskiyar lamari a kan hotunan.
Wakilin mu ya tuntuɓi shahararren jarumin, kuma ya tabbatar masa da cewa lallai aiki aka yi masa a idon sa ɗaya.
Da ya ke tattaunawa da mujallar Fim, jarumin ya ce, “Gaskiya ne, ido ɗaya ba lafiya, an yi mani ‘operation’, amma na samu sauƙi.
“Ranar Laraba, 16 ga Nuwamba, 2022 aka yi ‘operation’ ɗin, a Haske Specialist Hospital, Kaduna, da misalin ƙarfe 2:00 na rana.”
Ko me Balarabe Jaji zai ce wa masoyan sa game da damuwa da su ka yi don jin halin da ya ke ciki? Sai ya ce, “Allah ya saka wa kowa da alkhairi. An yi aiki, kuma aiki ya yi kyau, har an buɗe idon, na ga cigaba sosai. Saboda haka addu’a ya yi matuƙar tasiri, Allah ya saka masu da alkhairi.
“Aiki biyu aka yi a idon guda ɗaya, kuma an samu nasarar aikin, an yi shi ‘successfully’, saboda ‘yan’uwa sun taya ni addu’a ƙwarai.
“Don haka a yi min godiya wurin kowa da kowa. Allah ya ba kowa lafiya, waɗanda su ka rasu kuma a cikin mu, Allah ya gafarta masu, ya kuma yafe kurakuran su, mu kuma in tamu ta zo ya haɗa mu da su a Jannatul Firdausi.
“Iyalan da za mu bari a baya, Allah ka kula da su da kuma tarbiyyar su. Na gode ƙwarai da gaske.”
Comments 2