SHUGABAN ƙungiyar masu fassara finafinan Indiya zuwa Hausa na ƙasa, Malam Auwal Badi, ya bayyana cewa dokar nan da Hukumar Tace Finafinai Da Bidiyo ta Ƙasa (NFVCB) ta fitar ta haramcin sana’ar fassararrun finafinan za ta haifar da babbar matsala ga matasa.
Ya ce hakan ya sa tilas masu sana’ar da jami’an hukumar su zauna domin su samo mafita.
Badi ya faɗi haka ne a lokacin da ya ke tattaunawa da mujallar Fim a ofishin sa da ke Kasuwar Ƙofar Wambai a Kano.
Ya faɗa mana cewa, “Mun samu wannan umarni kamar yadda Hukumar Tace Finafinai ta Ƙasa ta fitar, amma a yanzu mu na kan zama da su ne, kuma na san za mu cimma matsaya kamar yadda mu ka saba yi a kan duk wasu al’amura idan su ka taso.
“Kuma ka sani, wannan wani abu ne da wasu su ka daɗe su na shirya mana maƙarƙashiya daga cikin mu.”
Shugaban ya ce harkar fassarar finafinan Indiya ba sabuwa ba ce, sun kai kusan shekara goma su na yin ta.
Ya ce masu yi wa harkar zagon ƙasa sun daɗe su na kai ƙarar su don su ga an hana su, amma ba su cimma nasara ba. “Sai kuma a yanzu su ka sake wata hanyar don ganin an hana mu kasuwancin mu,” inji shi.
Badi ya ƙara da cewa: “Ni na san ita hukuma ba za ta yi abin da zai cutar da ‘yan ƙasa ba, saboda haka a matsayin mu na ‘yan ƙasa mu na da damar mu yi kasuwancin mu yadda doka ta tsara.
“Don haka a yanzu ma mu na kan tattaunawa da hukumar tare da lauyoyin mu don ganin an samar da mafita.”
Shugaban ya yi nuni da cewa bai kamata gwamnati ta hana ɗimbin matasa sana’a ba saboda matsalar da hakan zai haifar.
Ya ce: “Babu yadda za a yi a hana sana’ar da mutane sama da dubu ɗari su ke cin abinci a cikin ta.
“Kuma mafi yawan masu wannan sana’ar za ka ga matasa ne, don haka idan har ka hana matasa sama da dubu ɗari sana’a a wannan lokacin, me ka ke ganin zai faru?”
Ya yi kira ga hukumar da ta duba matsalar da matasan za su iya fuskanta da kuma halin da ake ciki a ƙasar nan inda “mutane su na sana’ar ma a yanzu da yaya, ina ga idan aka ce an hana?”
Badi ya ce zama a tattauna a kan matsalar shi ne zai kawo ƙarshen lamarin.
“Domin a yanzu idan hukuma ta hana mu yin fassarar finafinan Indiya da kuma sayar da shi, to su kuma manyan gidajen talbijin da su ke fassarawa su na nunawa fa, su kuma yaya za a yi da su?
“Don haka ni ina ganin samar da tsari da kuma daidaito a tsakanin mu da Hukumar Tace Finafinai ta Ƙasa shi ne zai kawo mafita, ba hanawar ba.”
Idan an tuna, jami’in hukumar mai kula da shiyyar Arewa-maso-yamma, Alhaji Umar G. Fage, a wata hira da ya yi da mujallar Fim, ya bayyana dalilin hukumar na haramta yaɗa finafinan Indiya da aka fassaro.
A labarin da mu ka buga a ranar 16 ga Nuwamba, 2022, mun ruwaito shi ya na cewa haramcin ba sabo ba ne domin kuwa dokar Hukumar Tace Finafinai ta Ƙasa ta 1993 ta samar da shi.
Alhaji Umar ya ce akwai mutane da ke ƙorafi a kan “yadda wannan fassarar ta ke gurɓata al’adun mu da kuma yaren mu wanda za ka ji ana wasu kalamai na ɓata tarbiyya ko ɓata shi kan sa yaren na Hausa.”
Ya kuma yi nuni da cewa masana’antar Kannywood ta samu koma-baya ta dalilin wannan fassarar da ake yi, har ta kai kasuwancin finafinan Hausa ya durƙushe saboda zuwan fassarar Indiya.
Ya ce tilas ne hukumar sa ta yaƙi wannan fassarar, tunda da man haramtacciya ce, “don su na satar fasahar wasu ne su na sayarwa ba tare da haƙƙin su ba.”
Tuni dai hukumar ta shiga aikin kamen duk wanda ke sana’ar fassarar finafinan na Indiya, inda har ta cafke mutum uku, ta na kuma neman wasu mutum 14, waɗanda da zarar an kama su za a gurfanar da su a gaban kotu domin a yi masu shari’a.
![]()








Gaskiya Bama goyon bayan dakatar da fassara finafinan indiya zuwa Hausa…
Munfi samun nishaɗi da aka Acikin Wadannan Films, saɓanin na HAUSA..