JARUMIN Kannywood Adam A. Zango ya yi aure, kwanaki kaɗan bayan ya dawo Kaduna daga Kano inda ya yi jinya sakamakon haɗarin mota da ya yi.
An ɗaura masa auren a shekaranjiya Lahadi, inda ya auri sabuwar jaruma a Kannywood, mai suna Maimuna Musa.
Idan kun tuna, a farkon watan Yuni da ya gabata Zango ya yi mummunan haɗarin mota a hanyar sa ta zuwa Kano domin wasan Babban Sallah, har wata mace matashiya ta rasu a motar.
An kwantar da jarumin a asibiti tsawon lokaci, da aka sallame shi kuma ya ci gaba da yin jinya a Kano.
A makon jiya ya dawo gida Kaduna, kuma aka ɗaura masa aure.
Mujallar Fim ta ruwaito cewar ya yi wannan auren ne shekaru biyu da wata huɗu bayan rabuwar sa da matar sa ta shida da ya aura, wato Safiyya Umar Chalawa wadda suke da ‘ya ɗaya a tsakanin su.
Tun da ya dawo gida yake ta samun ɗimbin maziyarta daga sassa daban-daban na ƙasar nan, musamman ‘yan fim na Jihar Kaduna, masu zuwa yi masa jajen abin da ya faru.
Ɗaya daga cikin su, aminin da ne, Alhaji Yerima Shettima, wato shugaban Ƙungiyar Masu Ruwa da Tsaki ta Arewa (Northern Stakeholders Initiative, NSI).
Shettima da tawagar sun kai ziyarar dubiyar a jiya Litinin a gidan Zango da ke unguwar Barakallahu GRA da misalin ƙarfe 3:30 na yamma.


Su Yerima sun iske shi a falon sa, inda a nan aka yi masa addu’o’i na samun lafiya.
Yerima, wanda ɗan siyasa ne kuma mijin tsohuwar jarumar Kannywood Fati Ladan, ya jefi tsuntsu biyu da dutse ɗaya ne, domin bayan jajen, sai kuma ya taya shi murnar auren da ya yi.
Da yake jawabi yayin ziyarar, Yerima ya ce:
“Da mun san gaibu, ba za mu bari ka yi tafiyar nan ba domin har ɗaure ka zan sa a yi a gida na in ka ce sai ka tafi. Amma da yake lamari ne na Ubangiji, babu wanda ya isa ya ja. Sanin gaibu sai Allah.”
Ya ƙara da cewa, “Ana gobe za ka samu haɗarin, ka kai kusan goma na dare a gida na, har ina tunanin za ka zo wasan ƙwallon da za a yi a ranar, ashe tsautsayi ya kira ka. Allah ya ba ka lafiya.”
A nasa ɓangaren, Zango ya ce, “Ni kai na ba a ranar ya kamata in tafi ba. Amma haka Allah ya tsara lamarin sa. Ina godiya sosai da wannan ziyara, Allah ya saka da alkhairi, Allah ya bar zumunci. Na gode.”

Wasu daga cikin waɗanda suka je ziyarar sun haɗa da Alhaji Shehu Sani Sado, Mista Ɗanjuma Don J, Mista Yabo, Dakta Bashir Umar, Honarabul Aminu Monye, Honarabul Ibrahim PDP, Zaharaddeen Sani, Muhammad Ayuba (Karl Marx), Kwamared Sagir Umar, DJ Abdul, Nuhu Ɗanmani, Kwamared Mustapha, Ibrahim Alhassan, Ibrahim Auwal, Hajiya Maryam Masha, da Khadija Mukhtar.
![]()







