• Gida
  • Labarai da Rahotanni
    • Labarai
    • Rahotonni
    • Tattaunawa
  • Sharhi da Tsokaci
    • Sharhin Fim
    • Tsokaci
  • Masu Haskawa
    • Taurarin Fim
    • Marubuta
    • Mawaƙa
  • Addini da Rayuwa
    • Rayuwa
    • Iyalai
    • Al’adu
    • Addini
  • Ranar Murna
Wednesday, August 12, 2026
  • Login
Kannywood - News, reviews and more  › hausa
  • Gida
  • Labarai da Rahotanni
    • Labarai
    • Rahotonni
    • Tattaunawa
  • Sharhi da Tsokaci
    • Sharhin Fim
    • Tsokaci
  • Masu Haskawa
    • Taurarin Fim
    • Marubuta
    • Mawaƙa
  • Addini da Rayuwa
    • Rayuwa
    • Iyalai
    • Al’adu
    • Addini
  • Ranar Murna
No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai da Rahotanni
    • Labarai
    • Rahotonni
    • Tattaunawa
  • Sharhi da Tsokaci
    • Sharhin Fim
    • Tsokaci
  • Masu Haskawa
    • Taurarin Fim
    • Marubuta
    • Mawaƙa
  • Addini da Rayuwa
    • Rayuwa
    • Iyalai
    • Al’adu
    • Addini
  • Ranar Murna
No Result
View All Result
Kannywood - News, reviews and more  › hausa
No Result
View All Result
  • Gida
  • Labari
  • Addini
  • Al’adu
  • Iyali
  • Marubuta
  • Mawaƙa
  • Nijeriya
  • Ranar Murna
  • Rayuwa
  • Sharhin Fim
  • Tattaunawa
  • Taurari
  • Tsokaci

An yi jana’izar shugaban mawaƙan Kaduna Sani Ciyaman wanda ya rasu sanadiyyar ciwon hanta

by DAGA ABBA MUHAMMAD
September 22, 2021
in Labarai
1
An iso maƙabarta da gawar Sani Ciyaman

An iso maƙabarta da gawar Sani Ciyaman

0
SHARES
0
VIEWS
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsappShare on Telegram

A SAFIYAR yau aka yi jana’izar shugaban Ƙungiyar Mawaƙa ta Jihar Kaduna (NALSU) kuma memba a haɗaɗɗiyar ƙungiyar masu shirya finafinan Hausa ta Nijeriya (MOPPAN), Alhaji Muhammad Sani Shu’aibu (Ciyaman), wanda Allah ya yi wa rasuwa a daren jiya.

Mujallar Fim ta ruwaito cewa Sani Ciyaman ya rasu ne a gidan sa da ke Titin Maƙera, unguwar Rigasa, Kaduna, da misalin ƙarfe 7:30 na dare a jiya Talata, 21 ga Satumba, 2021.

Shekarun sa kimanin 39 a duniya.

Marigayi Sani ya rasu ya bar mahaifiya sa, da matar sa ɗaya da kuma ‘ya’ya huɗu duk mata.

Dandazon jama’ar da su ka halarci rufe Sani Ciyaman
Lokacin da ake ƙoƙarin saka Sani Ciyaman a cikin kushewar sa

Wakilin mu ya gano cewa marigayin ya ɗan kwana biyu ya na jinyar ciwon hanta, amma ba ya faɗa wa mutane. 

Hakan ya sa ba kowa ne ya san ba shi da lafiya ba, sai dai kawai labarin rasuwar sa ya riski mutane. 

Mutane sun kaɗu da jin labarin wannan babban rashi da aka yi domin kuwa Sani bango ne majinginar jama’a da dama, ba a iya ƙungiyar mawaƙan Jihar Kaduna ba, har ma ga Kannywood baki ɗaya.

An yi masa sallah a ƙofar gidan sa da misalin ƙarfe 8:30 na safe, daga nan aka wuce da shi maƙabartar unguwar, wadda ba ta da nisa daga gidan.

Ana jera itace a saman gawar mamacin a kabarin sa

Wasu daga cikin ‘yan fim da su ka halarci jana’izar sun haɗa da shi Maikano da Abubakar Yarima, Ali Baiti, Sagir Baban Kausar, Malam Yahaya Makaho, El-Mu’az Birniwa, Dikko Yakubu, Musa Mairabo, Ibrahim Ɗanguziri, M. Suraj, Sulaiman Sha’ani, Musa Aminu Carlos, Muktar SS, Murtala Aniya da MD Anas.

Bayan an rufe shi an dawo, sai tsohon shugaban MOPPAN na ƙasa, Alhaji Abdullahi Maikano Usman, ya tara dukkan ‘yan Kannywood da su ka halarci jana’izar, ya yi masu nasiha tare da jan hankali kan rayuwa. 

A cikin jawabin, Maikano ya ce, “Ya kamata mu yi wa kan mu faɗa, mu so junan mu, mu guji dukkan abin da bai da kyau, mu yi ƙoƙari wurin aikata ayyukan ƙwarai.” 

Jama’a su na addu’a a gaban kabarin Sani Ciyaman
Ali Baiti, Abubakar Yarim, El-Mu’az Muhammad Birniwa, Abdullahi Maikano da sauran jama’a cikin masallaci bayan an dawo daga maƙabarta

Ya ƙara da cewa: “Ya kamata mu yi ƙoƙari mu taimaki iyalan mamacin nan. Sannan ba sai mun yi a ƙungiyance ba, duk wanda Allah ya hore masa ko da N1,000 ne, ba na raina N1,000 ba ne, a’a wannan N1,000 ko N500 da ka bada za ka ga sakamakon da za ka samu a kan ta. Kuma idan za ka bada ba sai ka bari wani ya sani ba, ka yi tsakanin kai da Ubangijin ka, ba sai wani ya sani ba.” 

Mutane daga masana’antar fim da wajen ta sun ci gaba da tururuwa zuwa gidan mamacin domin yin ta’aziyya.

Allahu Akbar! Marigayi Alhaji Sani Shu’aibu (Ciyaman) a cikin mota

Daga cikin su akwai Hajiya Fatima Lamaj, wato shugabar MOPPAN reshen Jihar Kaduna a yanzu.

Allah ya jiƙan Sani Ciyaman, amin.

Loading

Tags: Abdullahi Maikano UsmanFatima Ibrahim Lamajhausa filmsKannywoodmawakan hausaMOPPANmutuwaNALSUSani Ciyaman
Previous Post

Zan gina cibiyar harkar finafinan Hausa a Nasarawa – Gwamna Sule

Next Post

Dokar hana yin fim kan aikata ta’asa: Afakallah ya biyo layin hauka, inji Falalu Ɗorayi

Related Posts

Tozali TV zai yi bikin Henna Ball da karrama masu ƙwazo da tallafa wa waɗanda suka tsira daga hare-hare a ranar 31 ga Oktoba
Labarai

Tozali TV zai yi bikin Henna Ball da karrama masu ƙwazo da tallafa wa waɗanda suka tsira daga hare-hare a ranar 31 ga Oktoba

August 8, 2026
Fitaccen mawaƙin siyasa Muhammadu Buhari ‘Kosan Waka’ ya kwanta dama
Labarai

Fitaccen mawaƙin siyasa Muhammadu Buhari ‘Kosan Waka’ ya kwanta dama

August 2, 2026
Yadda gwajin ƙwayoyin halitta na jini ya kawo ƙarshen auren Adam A. Zango da Maimuna Musa bayan watanni 11
Labarai

Yadda gwajin ƙwayoyin halitta na jini ya kawo ƙarshen auren Adam A. Zango da Maimuna Musa bayan watanni 11

August 1, 2026
Jami’an gwamnati sun yi zama da Kannywood domin fara aiwatar da shirin ba da inshorar lafiya kyauta ga ‘yan fim na Kano
Labarai

Jami’an gwamnati sun yi zama da Kannywood domin fara aiwatar da shirin ba da inshorar lafiya kyauta ga ‘yan fim na Kano

July 15, 2026
Kannywood tana buƙatar farfaɗo da gidajen sinima domin bunƙasa tattalin arzikin ƙirƙira – Sani Mu’azu
Labarai

Kannywood tana buƙatar farfaɗo da gidajen sinima domin bunƙasa tattalin arzikin ƙirƙira – Sani Mu’azu

July 14, 2026
A hira da mujallar Fim, mawaƙi Ado Gwanja ya aiko da saƙo ga masoyan sa daga gadon asibiti
Labarai

A hira da mujallar Fim, mawaƙi Ado Gwanja ya aiko da saƙo ga masoyan sa daga gadon asibiti

July 9, 2026
Next Post
Falalu A. Ɗorayi

Dokar hana yin fim kan aikata ta'asa: Afakallah ya biyo layin hauka, inji Falalu Ɗorayi

Comments 1

  1. Muhammad Lawal Hudu says:
    5 years ago

    ALLAH KAYIWA SANI CHAIRMAN RAHMA, KA KYAUTATA KWANCIYARSA YA ALLAH.

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

  • Home
  • Game Da Mu
  • Privacy Policy
  • Contact Us

© 2024 Mujallar Fim

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labari
  • Addini
  • Al’adu
  • Iyali
  • Marubuta
  • Mawaƙa
  • Nijeriya
  • Ranar Murna
  • Rayuwa
  • Sharhin Fim
  • Tattaunawa
  • Taurari
  • Tsokaci

© 2024 Mujallar Fim

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In
error: Content is protected !!