SHAHARARREN furodusa a Kannywood, Alhaji El-Sa’eed Yakubu Lere, zai ƙara aure a ranar Asabar mai zuwa.
Za a ɗaura auren sa da sahibar sa, Saudat Ibrahim Rigasa (Hajiyayye), a ranar Asabar, 8 ga Yuli, 2023 da misalin ƙarfe 11:00 na safe a gida mai lamba, E97, kan Titin Sabon Afaka, ‘Yankifi, Rigasa, Kaduna.

An tura katin gayyata a duk wani guruf na masana’antar Kannywood, inda ake gayyatar kowa da kowa.
Yakubu Lere zai zama sajen kenan, domin kuwa Hajiyayye ita ce matar sa ta uku.
Allah ya kai mu ranar da rai da lafiya, amin.
![]()







