BABBAN Bankin Nijeriya (CBN) ya ware wa masana’antar shirin fim da mawaƙa naira biliyan 22 don cin moriyar bashi mai sauƙi.
Daraktan sadarwa na bankin, Mista Isaac Okorafor, shi ne ya bayyana haka a yayin wani taron tattaunawa na haɗin gwiwa tare da masu ruwa da tsaki a kan manufofin shekaru biyar na bankin a ƙarshen mako a Uyo, babban birnin Jihar Akwa Ibom.
A jawabin sa, ya ce matakin ya ƙara ƙarfi ga masana’antar kamar yadda ta ɗauki jagorancin Afirka a gaba.
Ya ƙara da cewa matakin zai kuma lashi takobin yin fashin baƙi yayin da ya ke samar da dalilai na asali.
Okorafor ya ce bankin na CBN ya kuma yanke shawarar tayar da masana’antar, ya na faɗin, “A halin yanzu, Nollywood da Kannywood da masana’antar kaɗe-kaɗen Nijeriya su ne manyan masana’antar nishaɗi a Afirka. Ba za mu bar masana’antar ta faɗi ba.
“A shirye mu ke mu tara kuɗaɗen ‘yan fim da masu shirya finafinai a masana’antar.
“Kuma kasancewar Nijeriya na ɗaya daga cikin ƙasashen da ke da masana’antar ƙere-ƙere, za mu tallafa wa mutane a wannan fannin ma.
“Mun yanke hukuncin cewa dole ne mu farfaɗo da masana’antar. Mun fara ne ta hanyar bada tallafi ga manoman da su ka dasa auduga; mu na bayar da kuɗin ɗaukacin darajar, don duk wanda ya taka rawa, ciki har da masu amfani da sutura da masu yin sutura, don kada ta karye.
“Mu na yin hakan ne saboda idan tattalin arziƙin ƙasar ba ya aiki da kyau, CBN ba zai iya yin nasa aikin ba. Misali, a duk tsarin kuɗi da farashin kayayyaki, hauhawar farashin kayayyaki ba za ta iya zama kwanciyar hankali ba idan farashin abinci bai tsaya ba, saboda abinci ya fi yawa, sama da kashi 50 na abin da mu ke kashewa a Nijeriya.
“Idan mutane ba su da abincin da za su ci, yawan amfanin ƙasa ba zai ƙaru ba; idan mutane ba su da abinci da za su ci, lafiyar al’umma ba za ta iya zama ba.
“Haƙiƙa, lafiyayyen mutum ne wanda zai iya kawo ci-gaba, kuma ya kawo cigaban tattalin arziƙi, kuma a cikin yanayin da ba za a samar da ayyukan yi ba zai zama babu walwala, ma’aikata marasa aikin yi za su zama masu sauƙin kayan aiki a cikin hannun waɗanda su ka shirya guje wa laifi.”
![]()







