• Gida
  • Labarai da Rahotanni
    • Labarai
    • Rahotonni
    • Tattaunawa
  • Sharhi da Tsokaci
    • Sharhin Fim
    • Tsokaci
  • Masu Haskawa
    • Taurarin Fim
    • Marubuta
    • Mawaƙa
  • Addini da Rayuwa
    • Rayuwa
    • Iyalai
    • Al’adu
    • Addini
  • Ranar Murna
Friday, May 15, 2026
  • Login
Kannywood - News, reviews and more  › hausa
  • Gida
  • Labarai da Rahotanni
    • Labarai
    • Rahotonni
    • Tattaunawa
  • Sharhi da Tsokaci
    • Sharhin Fim
    • Tsokaci
  • Masu Haskawa
    • Taurarin Fim
    • Marubuta
    • Mawaƙa
  • Addini da Rayuwa
    • Rayuwa
    • Iyalai
    • Al’adu
    • Addini
  • Ranar Murna
No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai da Rahotanni
    • Labarai
    • Rahotonni
    • Tattaunawa
  • Sharhi da Tsokaci
    • Sharhin Fim
    • Tsokaci
  • Masu Haskawa
    • Taurarin Fim
    • Marubuta
    • Mawaƙa
  • Addini da Rayuwa
    • Rayuwa
    • Iyalai
    • Al’adu
    • Addini
  • Ranar Murna
No Result
View All Result
Kannywood - News, reviews and more  › hausa
No Result
View All Result
  • Gida
  • Labari
  • Addini
  • Al’adu
  • Iyali
  • Marubuta
  • Mawaƙa
  • Nijeriya
  • Ranar Murna
  • Rayuwa
  • Sharhin Fim
  • Tattaunawa
  • Taurari
  • Tsokaci

Cewar Umar Gombe game da rasuwar mahaifin sa: ‘Ina alfahari da shi sosai’

by DAGA ABBA MUHAMMAD
November 17, 2021
in Labarai
0
Marigayi Alhaji Sani Labaran

Marigayi Alhaji Sani Labaran

0
SHARES
0
VIEWS
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsappShare on Telegram

* Rasuwar Alhaji Sani Labaran babban rashi ne ga Jihar Gombe baki ɗaya, inji tsohon gwamna, Ibrahim Ɗanƙwambo

FITACCEN jarumi Umar Gombe ya bayyana cewa ya na alfahari da mahaifin sa, Alhaji Sani Labaran, wanda Allah ya yi rasuwa jiya.

Ya ce ya na alfahari da shi ne saboda ilimi da tarbiyyar da ya ba shi.

Haka kuma ya gode wa dukkan ‘yan fim da su ka yi masa ta’aziyya tare da yi wa mahaifin nasa addu’a.

Kamar yadda mujallar Fim ta bada labari jiya, Alhaji Sani Labaran ya rasu ne a jiyan, wato Talata, 16 ga Nuwamba, 2021, tare da bayyana cewa za a yi jana’izar sa a yau a Gombe.

Umar Gombe ya faɗa wa mujallar Fim cewa mahaifin nasa, wanda ɗan kimanin shekara 94 ne, ya rasu da misalin ƙarfe 4:05 na yamma a Asibitin Gwamnatin Tarayya, wato ‘Federal Medical Centre’, da ke garin Gombe, sakamakon ciwon ajali.

Marigayi Alhaji Sani Labaran (a hagu), tare da ɗan sa Umar Gombe
Marigayi Alhaji Sani Labaran (a hagu), tare da ɗan sa Umar Gombe
Marigayi Alhaji Sani Labaran tare da Dakta Ali Isa Pantami lokacin da ministan ya kai wa dattijon ziyara a gida

An yi jana’izar sa a yau Laraba da misalin ƙarfe 10:00 na safe a babban masallacin Juma’a da ke gidan Sarkin Gombe. 

Alhaji Labaran, wanda ya na daga cikin sanannun dattawan Jihar Gombe, ya rasu ya bar mata uku da ‘ya’ya 22, kuma Umar ne na 12 a cikin su.

Da wakilin mu ya tambayi jarumin abin da zai ce game da wannan babban rashi da ya yi, sai ya ce, “Ba na so in yi kuka, amma kamar wannan magana na so ta sa ni kuka. Ina fata kamar yadda mahaifi na ya jiƙai na a lokacin da na ke yaro har zuwa girma na, Allah ya jiƙan shi. 

“Kamar yadda na yi wa hira a baya, ina faɗa kullum ina alfahari da mahaifi na. Ina alfahari da shi sosai saboda ilimi da tarbiyyar da ya ba ni.”

Umar ya ƙara da cewa, “Alhamdu lillahi, na rayu rayuwa sosai da mahaifi na. Ya ilimantar da ni, ya tarbiyyatar da ni, kuma ya yi min komai na rayuwa. 

“Babu abin da zan ce sai dai in ce Allah ya jiƙan shi da rahama, ya kuma jiƙan sa kamar yadda ya jiƙai na ina yaro. 

“Haka kuma ina alfahari da ‘yan fim, kamar yadda na ke alfahari da ‘yan’uwa na. Domin idan ka duba tun daga ‘A to Z’ na Kannywood babu wanda bai ɗora hoton mahaifi na a shafin shi na soshiyal midiya ya yi masa addu’a ba, haka kuma babu wanda bai kira ni ta waya ya yi min ta’aziyya tare da yi wa mahaifi na addu’a. 

“Babu abin da zan ce masu sai godiya. Ku ma ina yi maku godiya.”

Tsohon gwamnan Jihar Gombe, Dakta Ibrahim Hassan Ɗanƙwambo, ya na daga cikin manyan mutanen jihar da su ka aika da saƙon ta’aziyya.

Ɗanƙwambo ya yi ta’aziyya kamar haka: “Inna Iillahi wa inna ilaihi raji’un! Abin da Allah ya bayar nashi ne, wanda ya karɓa ma nashi ne, kuma kowane ya na da ƙayyadadden lokaci a wajen Allah.

“Cikin alhini da tsananin kaɗuwa na samu labarin rasuwar ɗaya daga cikin dattawan mu na Jihar Gombe, Alhaji Sani Labaran, wanda Allah ya karɓi rayuwar sa a yammacin jiya Talata. 

“Marigayi Alhaji Sani Labaran dattijo ne wanda ya yi rayuwa abin koyi ga na baya, ya sadaukar da rayuwar sa wajen hidimta wa jama’a da kuma ƙoƙarin tabbatar da zaman lafiya da fahimtar juna a tsakanin al’umma. 

“Tabbas, rasuwar wannan dattijo babban rashi ne gare mu baki ɗaya. 

“A madadin ni kai na da iyalai na, ina miƙa ta’aziyyar mu ga iyalai da ‘yan’uwan wannan dattijo da sauran jama’ar Jihar Gombe baki ɗaya.

“Ina roƙon Allah (swt) ya jiƙan sa, ya gafarta masa, ya sa Aljannah Firdausi ce makomar sa. Ameen.”

A tasa ta’aziyyar, Ministan Sadarwa da Fasahar Zamani, Sheikh Isa Ali Pantami, ya faɗa cewa: “Allah Ya dauki rayuwar ɗaya daga cikin iyayen mu kuma aminin iyayen mu, a Jihar Gombe, shi ne Alhaji Sani Labaran. 

“Allah Ya gafarta masa, Ya masa rahama, Ya kyautata makwancin sa, da na sauran iyayen mu da malaman mu, da ‘ya’yan mu.

“Allah Ya kyautata namu bayan na su.”

Pantami ya wallafa saƙon ne a Facebook tare da hotuna guda huɗu da ya ɗauka da mamacin a falon sa, lokacin da ya kai wa shi Alhaji Sani wata ziyara a gida.

Dubban mutane sun ci gaba da yi wa marigayin addu’a.

Loading

Tags: Alhaji Sani LabaranDakta Ali Isa PantamiIbrahim Hassan DankwamboKannywoodmutuwaSarkin GombeUmar Gombe
Previous Post

Yanzu: Mahaifin jarumi Umar Gombe ya rasu

Next Post

Ni ɗan asalin Kano ne: Amsar Nuhu Abdullahi ga masu yi masa gorin asali

Related Posts

Rasuwar dattijon Kannywood, Nura Shareef, ta girgiza ‘yan fim
Labarai

Rasuwar dattijon Kannywood, Nura Shareef, ta girgiza ‘yan fim

February 22, 2026
Daraktar fim ta ƙi karɓar awad saboda kisan gillar da Isra’ila take yi a Gaza
Labarai

Daraktar fim ta ƙi karɓar awad saboda kisan gillar da Isra’ila take yi a Gaza

February 21, 2026
Fitaccen furodusa Kunle Afolayan ya yi haɗin gwiwa da Jamhuriyar Benin kan shirya finafinai
Labarai

Fitaccen furodusa Kunle Afolayan ya yi haɗin gwiwa da Jamhuriyar Benin kan shirya finafinai

February 19, 2026
An naɗa Farfesa Tengya matsayin sabon shugaban Cibiyar Koyon Finafinai ta Ƙasa
Labarai

An naɗa Farfesa Tengya matsayin sabon shugaban Cibiyar Koyon Finafinai ta Ƙasa

February 15, 2026
Alƙali ya ci Samha Inuwa tara ko ta je kurkuku wata 6
Labarai

Alƙali ya ci Samha Inuwa tara ko ta je kurkuku wata 6

February 13, 2026
Hukumar EFCC ta kama jarumar Kannywood, Samha Inuwa, saboda goge majina da takardun naira
Labarai

Hukumar EFCC ta kama jarumar Kannywood, Samha Inuwa, saboda goge majina da takardun naira

February 3, 2026
Next Post
Nuhu Abdullahi

Ni ɗan asalin Kano ne: Amsar Nuhu Abdullahi ga masu yi masa gorin asali

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

  • Home
  • Game Da Mu
  • Privacy Policy
  • Contact Us

© 2024 Mujallar Fim

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labari
  • Addini
  • Al’adu
  • Iyali
  • Marubuta
  • Mawaƙa
  • Nijeriya
  • Ranar Murna
  • Rayuwa
  • Sharhin Fim
  • Tattaunawa
  • Taurari
  • Tsokaci

© 2024 Mujallar Fim

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In
error: Content is protected !!