• Gida
  • Labarai da Rahotanni
    • Labarai
    • Rahotonni
    • Tattaunawa
  • Sharhi da Tsokaci
    • Sharhin Fim
    • Tsokaci
  • Masu Haskawa
    • Taurarin Fim
    • Marubuta
    • Mawaƙa
  • Addini da Rayuwa
    • Rayuwa
    • Iyalai
    • Al’adu
    • Addini
  • Ranar Murna
Monday, May 18, 2026
  • Login
Kannywood - News, reviews and more  › hausa
  • Gida
  • Labarai da Rahotanni
    • Labarai
    • Rahotonni
    • Tattaunawa
  • Sharhi da Tsokaci
    • Sharhin Fim
    • Tsokaci
  • Masu Haskawa
    • Taurarin Fim
    • Marubuta
    • Mawaƙa
  • Addini da Rayuwa
    • Rayuwa
    • Iyalai
    • Al’adu
    • Addini
  • Ranar Murna
No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai da Rahotanni
    • Labarai
    • Rahotonni
    • Tattaunawa
  • Sharhi da Tsokaci
    • Sharhin Fim
    • Tsokaci
  • Masu Haskawa
    • Taurarin Fim
    • Marubuta
    • Mawaƙa
  • Addini da Rayuwa
    • Rayuwa
    • Iyalai
    • Al’adu
    • Addini
  • Ranar Murna
No Result
View All Result
Kannywood - News, reviews and more  › hausa
No Result
View All Result
  • Gida
  • Labari
  • Addini
  • Al’adu
  • Iyali
  • Marubuta
  • Mawaƙa
  • Nijeriya
  • Ranar Murna
  • Rayuwa
  • Sharhin Fim
  • Tattaunawa
  • Taurari
  • Tsokaci

Da Ban San Shi Ba

by MUHAMMAD LAWAN PRP
January 8, 2017
in Marubuta
0
Fauziyya D. Sulaiman da littafin ta na 'Da Ban San Shi Ba'

Fauziyya D. Sulaiman da littafin ta na 'Da Ban San Shi Ba'

0
SHARES
0
VIEWS
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsappShare on Telegram

LITTAFI:  Da Ban San Shi Ba
MARUBUCIYA: Fauziyya D. Sulaiman
KAMFANI: Abin Yabo Publishing Company, Kano
SHAFUKA: 152
FARASHI: N200
SHEKARA: 2016
ISBN:  BABU

Fauziyya D. Sulaiman sananniya ce kuma shahararriyar marubuciyar da za a iya kira lamba daya a mata marubuta na wannan zamanin. Bayan rubutun littafi, marubuciyar finafinan Hausa ce, sannan ma’aikaciya ce a gidan talabijin na Arewa24 da ke Kano.

LABARI

‘Da Ban San Shi Ba’ labarin wani yaro ne Aliyu da aka kawo shi almajiranci a birni daga kauyen su Sambauna. Bayan ya sha wahala irin ta almajiranci sai tsautsayi da tsananin wahala ta rayuwa ta sa shi zuwa wurin wani gardi a tasha, wanda ya nemi bata masa rayuwa ta hanyar neman maza. A dole Aliyu ya gudu ya sha da kyar, ya fadi a kofar gidan wani mutum a sume. Da safe mutumin, mai suna Alh. Musa, ya tsince shi ya kuma taimaka masa.

Alh. Musa na da mata, Hajiya Bilkisu, da ‘ya mai suna Hanan. Ya rike Aliyu da amana, ya saka shi a makarantar addini da ta zamani har ya zama mutum ya kammala digirin sa. Sai dai Hajiya Bilkisu da Hanan sun tsani Aliyu matuka, su na cewa almajiri ne, su kuma ‘yan gayu.
Alh. Musa ya nada Aliyu a matsayin manaja, ya gina masa gida, sannan ya wanke ‘yar sa zai ba shi.

A nan fa aka fara cakwakiya, domin bayan tsanar da Hanan ke yi wa Aliyu akwai saurayin da ta ke so (Mansur), wani baduniyi wanda ya yi karatu a Turai.

A gefe kuma wata budurwa ‘yar wani attajiri (Fa’iza) ta dage Aliyu ta ke so, yayin da shi kuma bai damu da ita ba. Cikin kankanin lokaci ya tsinci kan sa a soyayyar Hanan ba tare da ya sani ba.

Alh. Musa kuma ya dage kan lallai Aliyu ne zai auri Hanan, domin ya yi kama da dan sa da ya yi hadari ya mutu tare da mahaifiyar sa.

WARWARAR JIGO

– Labarin ya fito da illar kai yara kanana almajiranci, domin da Aliyu ya biye wa son zuciya da ya tsinci kan sa a mummunar hanya.

– An nuna amfanin taimaka wa wanda ya ke cikin wani hali, kamar yadda Alh. Musa ya yi.

– Biye wa son zuciya da bijire wa iyaye ba shi da alfanu, kamar yadda Hanan ta yi, daga baya ta kwana nadama.

SALO

Marubuciyar ta yi amfani da mkakken salo ne ta hanyar da zai kayatar. Hausar littafin mai saukin fahimta ce. Haka kuma taurari da garuruwan labarin sun dace da labarin sosai. Akwai rike tunanin mai karatu ta yadda labarin zai ba shi sha’awa.

ZUBI DA TSARI

An zubo labarin ne bisa amfani da karin magana da salon magana, zubin da ba kowanne marubuci ba ne ke iyawa. Haka tsarin labarin ya tafi tiryan-tiryan ba karaya, ta yadda ba zai gimshi mai karatu ba.

KA’IDOJIN RUBUTU

An kiyaye ka’idojin rubutu a littafin, duk da yake a wasu wuraren an rika rubuta wata kalma ba daidai ba (abin da marubutan ke kira typing error).

KKURAKURAI

1. Shafi na 3 littafi na 1: “… su na barar tumun dawa…” Ba a cewa tumun dawa sai dai tumun gero.

2. A shafi na 27 littafi na 1: Marubuciyar ta ambaci “garken akuyoyi” maimakon “garken awaki”.

3.  Littafi na 1 shafi na 56: Marubuciyar ta ce, ran Alu ya rabu da gangar jikin sa, wato ‘ya mutu’, amma a shafi na 58 sai ga shi Alu ya farfado. Da ma ana mutuwa a dawo?  Ina ma dai cewa ta yi,  ‘…ran shi ya rabu da gangar jikin sa na wucin-gadi.’

4. A wajen zubin labarin an maimaita taken, ‘KOWA YA BAR GIDA,’  maimakon a samar da wani taken a matsayin ci-gaban labarin. Duba shafi na 11  da 35  littafi na 2.

5. Canjin suna daga shafi na 41 zuwa na 42 a littafi na 2: Lokacin da Rabe ya ke ba wa Aliyu labarin bayan rabuwar su, ya ce ya hadu da wani almajiri Baba, amma sai sunan Buba ya koma Ilu.

6. Duk da yake jigon labarin ya na nuna illar kai yara almajiranci, amma marubuciyar ta bar kashi casa’in cikin dari na labarin ya koma kan soyayya.

7. A littafi na 3 shafi na 107: ‘Yan fashi sun shiga gidan makwabtan Aliyu da Hanan, sai aka ce Hanan ta ji karar harbi… har kuma harsashi ya fado gidan su. Daga baya marubuciyar ta ce sun kashe mai gidan ne kawai. A yanayin wurin ya fi kama da musayar wuta da ‘yan sanda, saboda harbin ya yi yawa.

8. A shafi na 109 littafi na 3: Marubuciyar ta ce ‘yan fashin sun kashe mai gidan kadai, amma a can gaba sai ta ce “an fita da gawarwakin zuwa makwancin su.” Shin mutum nawa aka kashe?

9. A shafi na 87 littafi na 4: Sunan mahaifiyar Mansur Zaituna, amma a shafi na 125 sai ga shi sunan ta ya koma Haj. Bahijja. Ko ya aka haihu a ragaya?

10. Abu ne mawuyaci a saka ranar auren Aliyu da Fa’iza har kuma a yi biki ta tare da wata guda ba tare da ta san labarin rabuwar Aliyu da matar sa ba. Duba shafi na 87, littafi na 4.

11.  Babu inda aka rubuta kalmar ‘yarda’  daidai a gaba daya littafin daidai, sai dai ‘yadda’. Wadannan kalmomi su na da bambanci a jimlace.

A gaida hazikar marubuciya.

Loading

Previous Post

Yadda Na Ke Rera Waka Ba Tare Da Karantawa Ba — Malam Yahaya Makaho

Next Post

Waƙar Ta’aziyyar Mallam Mu’azu Haɗejia ta Alhaji Mudi Sipikin

Related Posts

Taron Ranar Marubuta Hausa ta Duniya: Sanarwar Bayan Taro
Marubuta

Taron Ranar Marubuta Hausa ta Duniya: Sanarwar Bayan Taro

January 10, 2026
Taron Ranar Marubutan Hausa ta Duniya ya gabato, shirye-shirye sun kankama
Marubuta

Taron Ranar Marubutan Hausa ta Duniya ya gabato, shirye-shirye sun kankama

December 25, 2025
‎Sanata Shehu Sani ya ba gwarazan gasar Hikayata kyautar miliyan ɗaya a taron liyafa
Marubuta

‎Sanata Shehu Sani ya ba gwarazan gasar Hikayata kyautar miliyan ɗaya a taron liyafa

December 25, 2025
Ban san farin ciki yana hana barci ba sai da aka ce ni ce ta ɗaya a gasar Hikayata – Fadila Lamiɗo
Marubuta

Ban san farin ciki yana hana barci ba sai da aka ce ni ce ta ɗaya a gasar Hikayata – Fadila Lamiɗo

December 24, 2025
Buri na shi ne saƙonnin da suke cikin rubutu na su zama masu tasiri ga al’umma – Hauwa Shehu
Marubuta

Buri na shi ne saƙonnin da suke cikin rubutu na su zama masu tasiri ga al’umma – Hauwa Shehu

December 19, 2025
Gidauniya ta ƙaddamar da littattafai biyu domin inganta rayuwar mata
Marubuta

Gidauniya ta ƙaddamar da littattafai biyu domin inganta rayuwar mata

December 8, 2025
Next Post
Daga hagu: Alhaji Mudi Sipikin (1930-2013) da Malam Mu'azu Haɗejia (1918-1958)

Waƙar Ta'aziyyar Mallam Mu'azu Haɗejia ta Alhaji Mudi Sipikin

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

  • Home
  • Game Da Mu
  • Privacy Policy
  • Contact Us

© 2024 Mujallar Fim

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labari
  • Addini
  • Al’adu
  • Iyali
  • Marubuta
  • Mawaƙa
  • Nijeriya
  • Ranar Murna
  • Rayuwa
  • Sharhin Fim
  • Tattaunawa
  • Taurari
  • Tsokaci

© 2024 Mujallar Fim

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In
error: Content is protected !!