TSOHON Mataimakin Shugaba (wato Vice-Chancellor) na Buɗaɗɗiyar Jami’ar Nijeriya (NOUN), Farfesa Abdalla Uba Adamu, ya bayyana cewa da yana da hali, da ya ba jarumin Kannywood, Abba El-Mustapha, digirin digirgir.
Farfesa Abdalla ya faɗi haka ne cikin wata sanarwa da aka fitar a yau domin yin ƙarin bayani kan jinjinawar da ya yi wa El-Mustapha, wanda shi ne Shugaban Hukumar Tace Finafinai da Ɗabi’i ta Jihar Kano, a wurin taron karrama tsofaffin ‘yan fim da ƙungiyar Kannywood Family ta shirya a Kano a shekaranjiya Litinin.
A taron bikin karramawar, lokacin da aka kira shi ya ba shugaban hukumar garkuwar karramawar sa, sai mashahurin malamin ya kira shi da ‘Dakta Abba El-Mustapha’.
Mujallar Fim ta ruwaito cewa bayan taron, an ga buƙatar a yi ƙarin bayani ganin cewa Hukumar Tace Finafinai ta Jihar Kano ta wallafa wani bidiyo a soshiyal midiya inda ta ambato El-Mustapha yana faɗin cewa Farfesa Abdalla ya jaddada masa da digirin digirgir.
Shi kuwa a ɓangaren sa, malamin jami’ar ya kafa hujja ne da yawan ayyukan da El-Mustapha ya yi a Kannywood da kuma tasirin su a cikin al’ummar Jihar Kano.

A ƙarin bayanin, Farfesan ya nuna cewa ba fa digiri ya ce ya ba Abba ba, don kada a lanƙwasa gajeren jawabin da ya yi a taron da wata manufa daban.
Ya ce, “Ni ba ni da ikon da zan ba wa kowa digiri, wannan aikin Majalisar Dattijai ne ta jami’io’i. Amma na san a waɗansu ƙasashen a Turai akan gayyaci mutum ya gabatar da ayyukan sa, watau rubuce-rubuce, ko kuma waɗansu ayyukan basira, a ɗora su a bisa ma’aunin cancanta, a kira shi a ce ya kare.
“Idan ya yi haka, aka gamsu, to ana ba shi doctorate na yaba wa basirar sa.
“To ni manazarci ne fiye da shekaru 25 a masana’antar Kannywood, kuma a kan ido na Abba El-Mustapha ya zama gwarzon finafinai.
“To idan da za a ba ni dama in yi masa jarrabawa, tabbas zan yi masa kuma in ba shi doctorate saboda yawa, inganci da kuma muhimmancin finafinan da ya yi alaƙa da su.
“Saboda haka ne ma nake kiran sa da ‘Dr’ Abba El-Mustapha.
“Sannan kuma ya taka rawar gani a yanzu wajen kawo gyara a masana’antar nishaɗi a Kano ta yadda yanzu an fara gane inda aka nufa. Wannan ma abin yabo ne.”
Shi dai Abdalla Uba Adamu, Farfesa ne a kan tuddan nazari biyu, wato Sashen Kimiyyar Ilimi (Science Education) da nazarin Yaɗa Labarai da Al’adu (Media and Cultural Studies).
Ya koyar a jami’o’i a cikin da wajen Nijeriya, wato har a Amurka da wasu ƙasashen nahiyar Turai.
A yanzu yana sahu na gaba, ko ma a ce masa liman, a fagen nazarin harkar finafinan Hausa.
![]()







