BABBAN Sakataren Hukumar Tace Finafinai da Ɗab’i ta Jihar Kano, Alhaji Abba El-Mustapha, ya miƙa saƙon ta’aziyyar sa ga tsohon Shugaban hukumar, Alhaji Isma’ila Na-Abba Afakallahu, na rasuwar mahaifiyar sa.
Saƙon ta’aziyyar mai ɗauke da sa hannun jami’in hulɗa da jama’a hukumar, Malam Abdullahi Sani Sulaiman, ta ce, “Inna lillahi wa inna ilaihir raji’un. Tabbas dukkan rai sai ta ɗanɗani mutuwa.”
Malam Abdullahi ya ce, “Babban Sakataren Hukumar Tace Finafinai ta Jihar Kano, Alhaji Abba El-Mustapha, ya bayyana baƙin cikin sa tare da nuna alhini ga tsohon shugaban Hukumar Tace Finafinai ta Jihar Kano Malam Isma’ila Na-Abba Afakallah a kan rashin mahaifiyar sa, Hajiya Gwaggo, wacce ta rasu yau bayan rashin lafiya.”
El-mustapha ya bayyana marigayiyar a matsayin uwa tagari kuma abin koyi.
Ya ce rashin ya zama ba za a iya maye gurbin ta ba, ba wai ga dangin ta kaɗai ba, har ma da ɗaukacin al’ummar Musulmi.
Shugaban ya kuma roƙi Allah maɗaukakin Sarki da ya yafe mata dukkan zunuban ta, Aljannatul Firdausi ta zama mazaunin ta na ƙarshe.
Daga ƙarshe ya yi addu’a ga Allah maɗaukakin Sarki da ya bai wa ‘yan’uwan ta ƙarfin gwiwar jure rashin ta.
Kamar yadda mujallar Fim ta ruwaito tun da fari, Hajiya Fatima Mu’azu (Gwaggo) ta rasu ne a yau a Kano sakamakon rashin lafiya.
Shekarun ta 97.
![]()







