• Gida
  • Labarai da Rahotanni
    • Labarai
    • Rahotonni
    • Tattaunawa
  • Sharhi da Tsokaci
    • Sharhin Fim
    • Tsokaci
  • Masu Haskawa
    • Taurarin Fim
    • Marubuta
    • Mawaƙa
  • Addini da Rayuwa
    • Rayuwa
    • Iyalai
    • Al’adu
    • Addini
  • Ranar Murna
Tuesday, August 25, 2026
  • Login
Kannywood - News, reviews and more  › hausa
  • Gida
  • Labarai da Rahotanni
    • Labarai
    • Rahotonni
    • Tattaunawa
  • Sharhi da Tsokaci
    • Sharhin Fim
    • Tsokaci
  • Masu Haskawa
    • Taurarin Fim
    • Marubuta
    • Mawaƙa
  • Addini da Rayuwa
    • Rayuwa
    • Iyalai
    • Al’adu
    • Addini
  • Ranar Murna
No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai da Rahotanni
    • Labarai
    • Rahotonni
    • Tattaunawa
  • Sharhi da Tsokaci
    • Sharhin Fim
    • Tsokaci
  • Masu Haskawa
    • Taurarin Fim
    • Marubuta
    • Mawaƙa
  • Addini da Rayuwa
    • Rayuwa
    • Iyalai
    • Al’adu
    • Addini
  • Ranar Murna
No Result
View All Result
Kannywood - News, reviews and more  › hausa
No Result
View All Result
  • Gida
  • Labari
  • Addini
  • Al’adu
  • Iyali
  • Marubuta
  • Mawaƙa
  • Nijeriya
  • Ranar Murna
  • Rayuwa
  • Sharhin Fim
  • Tattaunawa
  • Taurari
  • Tsokaci

Gasar Ahmad Ɗangiwa: An yi wa zakaru 30 bita

by DAGA ZAIDU BARMO
August 16, 2020
in Marubuta
0
Mahalarta bitar a Katsina bayan an tashi daga taron

Mahalarta bitar a Katsina bayan an tashi daga taron

0
SHARES
0
VIEWS
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsappShare on Telegram
Arc. Ahmad Musa Ɗangiwa
Literary Competition 2019 
(Gasar Gajerun Labaran Hausa) 
 
RAHOTO DANGANE DA TARON BITAR DA AKA YI TA MUTANE 30
WANDA AKA GUDANAR A MUNAJ EVENTS CENTRE, KATSINA, A RANAR 15 GA AGUSTA, 2020
 
AN fara yi wa gwarazan gasar su 30 rajista wanda Malam Mustapha Kabir ya yi, inda kowa ya rubuta sunan sa lambar wayar sa da sunan labarin sa, da jihar sa. An kuma raba wa mahalarta taron littafi, ‘face mask’, biro, jakunkuna duk masu ɗauke da tambarin gasar. 
 
Kabir Sa’idu Bahaushe ne kakakin taron. Bayan gabatar da manyan baƙi, an ba kowa damar gabatar da kan sa da labarin sa.
 
Daga nan shugaban taron, Yazid Nasudan, ya yi taƙaitaccen jawabin buɗewa.
 
Daga nan ne kuma ‘yan taro su ka saurari jawabi daga manajan bankin bada lamuni, reshen Jihar Katsina, Alhaji Rabi’u Ali, a kan bada lamunin gina gidaje na ƙasa.
 
‘Yan taro sun karya kumallo, daga nan aka yi tambayoyi dangane da bankin bada lamunin gina gidaje na ƙasa.
 
Malam Hamza S. Usman ya gabatar da jawabi a kan abin da ya kamata marubuci ya kula da su kafin labarin sa ya cika sharuɗɗan nazari.
 
Mata marubuta a lokacin gudanar da bitar
 
Bayan gama jawabin sa, an ba masu sauraro damar su yi tambayoyi game da jawabin da Malam Hamza ya gabatar.
 
Injiniya Suraj Yazeed Abukur, Manajan Daraktan hukumar kula da hanyoyi ta Jihar Katsina (KASROMA), ya gabatar da maƙala a kan abubuwan da ya kamata marubuci ya lura da su yayin da ya ke magana a kan matsalolin gine-gine. Jawabai ne ya yi waɗanda duk marubucin da zai yi labari a kan gini tabbas ya na buƙatar su, matuƙar dai ya na son ya yi rubutu mai inganci.
 
Shi ma kamar na baya, ‘yan taro sun yi tambayoyi a kan abubuwan da ba su gane ba ko su ke son sani game da jawabin da ya yi. An yi tambayoyi masu ma’ana kuma ya amsa. 
 
Ado Ahmad Gidan Dabino ya gabatar da maƙalar sa “Matakan Rubuta Gajerun Labarai”, wadda ta ƙunshi menene gajeren labari? Yadda ake rubuta ƙayataccen labari bisa doron matakai, inda har ya kawo wasu matakai guda bakwai da duk marubucin da ke son labarin sa ya inganta ya kamata ya bi.
 
Wani sashe na mahalartan bitar
 
‘Yan taro sun yi tambayoyi, kuma sun samu gamsasshiyar amsa.
 
Daga nan aka ci abincin rana, aka ba mahalartan su 30 satifiket da kuɗaɗe waɗanda za su riƙe. 
 
* Zaidu Barmo shi ne jami’in yaɗa labarai na kwamitin shirya gasar
“Arc. Ahmad Musa Dangiwa Literary Competition 2020”

Loading

Previous Post

Mas’alar fyaɗe da taɓarɓarewar tarbiyya a ƙasar mu

Next Post

Shekara a kujera: Minista Sadiya ta jinjina wa ‘yan jarida da ma’aikatan agaji

Related Posts

Taron Ranar Marubuta Hausa ta Duniya: Sanarwar Bayan Taro
Marubuta

Taron Ranar Marubuta Hausa ta Duniya: Sanarwar Bayan Taro

January 10, 2026
Taron Ranar Marubutan Hausa ta Duniya ya gabato, shirye-shirye sun kankama
Marubuta

Taron Ranar Marubutan Hausa ta Duniya ya gabato, shirye-shirye sun kankama

December 25, 2025
‎Sanata Shehu Sani ya ba gwarazan gasar Hikayata kyautar miliyan ɗaya a taron liyafa
Marubuta

‎Sanata Shehu Sani ya ba gwarazan gasar Hikayata kyautar miliyan ɗaya a taron liyafa

December 25, 2025
Ban san farin ciki yana hana barci ba sai da aka ce ni ce ta ɗaya a gasar Hikayata – Fadila Lamiɗo
Marubuta

Ban san farin ciki yana hana barci ba sai da aka ce ni ce ta ɗaya a gasar Hikayata – Fadila Lamiɗo

December 24, 2025
Buri na shi ne saƙonnin da suke cikin rubutu na su zama masu tasiri ga al’umma – Hauwa Shehu
Marubuta

Buri na shi ne saƙonnin da suke cikin rubutu na su zama masu tasiri ga al’umma – Hauwa Shehu

December 19, 2025
Gidauniya ta ƙaddamar da littattafai biyu domin inganta rayuwar mata
Marubuta

Gidauniya ta ƙaddamar da littattafai biyu domin inganta rayuwar mata

December 8, 2025
Next Post
Hajiya Sadiya Umar Farouq

Shekara a kujera: Minista Sadiya ta jinjina wa 'yan jarida da ma'aikatan agaji

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

  • Home
  • Game Da Mu
  • Privacy Policy
  • Contact Us

© 2024 Mujallar Fim

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labari
  • Addini
  • Al’adu
  • Iyali
  • Marubuta
  • Mawaƙa
  • Nijeriya
  • Ranar Murna
  • Rayuwa
  • Sharhin Fim
  • Tattaunawa
  • Taurari
  • Tsokaci

© 2024 Mujallar Fim

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In
error: Content is protected !!