Ma’aikatar Sana’a, Masana’antu da Zuba Jari ta Tarayya tare da Sarkin Musulmi, Alhaji Muhammadu Sa’ad Abubakar III, sun amince wa Hajiya Rahma Abdulmajid ta shirya wani fim kan rayuwa da tsatson fitacciyar malama kuma marubuciyar nan, Gimbiya Nana Asma’u ‘yar Mujaddadi Shehu Usmanu Ɗanfodiyo.
Rahma, wadda ita ce Mai Taimaka wa Shugaban Ƙasa kan Harkokin Rediyo da Watsa Labarai a Ofishin Mataimakin Shugaban Ƙasa, za ta yi fim ɗin a ƙarƙashin kamfanin Script Plus Limited.
Ana sa ran fim ɗin zai hasko rawar abar yabo da gudunmawar da Nana Asma’u ta bayar a Daular Usmaniyya wajen cigaban ilimi, ƙarfafa mata da kuma ilimin addinin Musulunci.
A cikin wata wasiƙa mai ɗauke da ranar 21 ga Nuwamba, 2025, Sarkin Musulmi, ta hannun Sakataren Majalisar Masarautar Sakkwato, Alhaji Sa’idu Muhammadu Maccido, ya isar da izinin majalisar ga aikin fim ɗin ga Rahma Abdulmajid.
Takardar ta ce: “Mun yi farin cikin jin cewa kun ɗauki nauyin shirya fim kan Nana Asma’u ‘yar Usman Ɗanfodiyo, wadda ga mutane da dama ita ce ainihin misalin mace Musulma a Afirka… Majalisar Masarauta na isar da amincewar ta ga wannan aiki tare da ba ku damar fara shi kamar yadda kuka nemi izini.”
Majalisar ta nemi a dinga ba ta rahotanni lokaci zuwa lokaci da kuma damar shiga nazarin ƙarshe na fim ɗin kafin a ƙaddamar da shi.
Ita ma Ma’aikatar Masana’antu, Sana’a da Zuba Jari ta Tarayya, ta hannun Sashen Dokokin Kasuwanci, ta tabbatar da amincewar ta ta wata wasiƙa mai shaida, dangane da neman rajistar wannan aiki a matsayin alamar kasuwanci (trademark).
Babbar Furodusar fim ɗin, Rahma Abdulmajid, ta ce hangen nesan aikin ya wuce Arewa, domin al’adun sa masu yalwa za su ƙara haɗin kai da wanzar da zaman lafiya a faɗin ƙasar nan.
Ta ce: “Wannan labari ne mai muhimmanci na jagoranci, ban-gaskiya da ilimi wanda ya shafi dukkan ‘yan Najeriya.
“Ta hanyar fito da tushen ilimi da halayyar kirki da manyan mutane irin su Nana Asma’u suka kafa, muna ƙoƙarin amfani da wannan kyakkyawan tarihi domin ƙara haɗin kai da wanzar da zaman lafiya tsakanin Hausa-Fulani da sauran ƙabilu a Arewa da kuma ƙasa baki ɗaya.
“Rayuwar Nana Asma’u na bayar da hujjar tarihi mai ƙarfi cewa ilimin mata ya taɓa daɗewa yana cikin al’ada da darajar addini a Arewa, ba wani abu ne da aka shigo da shi daga waje ba.”
![]()







