• Gida
  • Labarai da Rahotanni
    • Labarai
    • Rahotonni
    • Tattaunawa
  • Sharhi da Tsokaci
    • Sharhin Fim
    • Tsokaci
  • Masu Haskawa
    • Taurarin Fim
    • Marubuta
    • Mawaƙa
  • Addini da Rayuwa
    • Rayuwa
    • Iyalai
    • Al’adu
    • Addini
  • Ranar Murna
Wednesday, August 26, 2026
  • Login
Kannywood - News, reviews and more  › hausa
  • Gida
  • Labarai da Rahotanni
    • Labarai
    • Rahotonni
    • Tattaunawa
  • Sharhi da Tsokaci
    • Sharhin Fim
    • Tsokaci
  • Masu Haskawa
    • Taurarin Fim
    • Marubuta
    • Mawaƙa
  • Addini da Rayuwa
    • Rayuwa
    • Iyalai
    • Al’adu
    • Addini
  • Ranar Murna
No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai da Rahotanni
    • Labarai
    • Rahotonni
    • Tattaunawa
  • Sharhi da Tsokaci
    • Sharhin Fim
    • Tsokaci
  • Masu Haskawa
    • Taurarin Fim
    • Marubuta
    • Mawaƙa
  • Addini da Rayuwa
    • Rayuwa
    • Iyalai
    • Al’adu
    • Addini
  • Ranar Murna
No Result
View All Result
Kannywood - News, reviews and more  › hausa
No Result
View All Result
  • Gida
  • Labari
  • Addini
  • Al’adu
  • Iyali
  • Marubuta
  • Mawaƙa
  • Nijeriya
  • Ranar Murna
  • Rayuwa
  • Sharhin Fim
  • Tattaunawa
  • Taurari
  • Tsokaci

Gwamnatin Tarayya da Sarkin Musulmi sun amince wa Rahma Abdulmajid ta shirya fim kan Nana Asma’u ‘yar Shehu Ɗanfodiyo

by ALI KANO
November 26, 2025
in Labarai
0
Gwamnatin Tarayya da Sarkin Musulmi sun amince wa Rahma Abdulmajid ta shirya fim kan Nana Asma’u ‘yar Shehu Ɗanfodiyo

Mai Alfarma Sarkin Musulmi, Alhaji Sa'ad Abubakar III, da Hajiya Rahma Abdulmajid

0
SHARES
0
VIEWS
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsappShare on Telegram

Ma’aikatar Sana’a, Masana’antu da Zuba Jari ta Tarayya tare da Sarkin Musulmi, Alhaji Muhammadu Sa’ad Abubakar III, sun amince wa Hajiya Rahma Abdulmajid ta shirya wani fim kan rayuwa da tsatson fitacciyar malama kuma marubuciyar nan, Gimbiya Nana Asma’u ‘yar Mujaddadi Shehu Usmanu Ɗanfodiyo.

Rahma, wadda ita ce Mai Taimaka wa Shugaban Ƙasa kan Harkokin Rediyo da Watsa Labarai a Ofishin Mataimakin Shugaban Ƙasa, za ta yi fim ɗin a ƙarƙashin kamfanin Script Plus Limited.

Ana sa ran fim ɗin zai hasko rawar abar yabo da gudunmawar da Nana Asma’u ta bayar a Daular Usmaniyya wajen cigaban ilimi, ƙarfafa mata da kuma ilimin addinin Musulunci.

A cikin wata wasiƙa mai ɗauke da ranar 21 ga Nuwamba, 2025, Sarkin Musulmi, ta hannun Sakataren Majalisar Masarautar Sakkwato, Alhaji Sa’idu Muhammadu Maccido, ya isar da izinin majalisar ga aikin fim ɗin ga Rahma Abdulmajid.

Takardar ta ce: “Mun yi farin cikin jin cewa kun ɗauki nauyin shirya fim kan Nana Asma’u ‘yar Usman Ɗanfodiyo, wadda ga mutane da dama ita ce ainihin misalin mace Musulma a Afirka… Majalisar Masarauta na isar da amincewar ta ga wannan aiki tare da ba ku damar fara shi kamar yadda kuka nemi izini.”

Majalisar ta nemi a dinga ba ta rahotanni lokaci zuwa lokaci da kuma damar shiga nazarin ƙarshe na fim ɗin kafin a ƙaddamar da shi.

Ita ma Ma’aikatar Masana’antu, Sana’a da Zuba Jari ta Tarayya, ta hannun Sashen Dokokin Kasuwanci, ta tabbatar da amincewar ta ta wata wasiƙa mai shaida, dangane da neman rajistar wannan aiki a matsayin alamar kasuwanci (trademark).

Babbar Furodusar  fim ɗin, Rahma Abdulmajid, ta ce hangen nesan aikin ya wuce Arewa, domin al’adun sa masu yalwa za su ƙara haɗin kai da wanzar da zaman lafiya a faɗin ƙasar nan.

Ta ce: “Wannan labari ne mai muhimmanci na jagoranci, ban-gaskiya da ilimi wanda ya shafi dukkan ‘yan Najeriya.

“Ta hanyar fito da tushen ilimi da halayyar kirki da manyan mutane irin su Nana Asma’u suka kafa, muna ƙoƙarin amfani da wannan kyakkyawan tarihi domin ƙara haɗin kai da wanzar da zaman lafiya tsakanin Hausa-Fulani da sauran ƙabilu a Arewa da kuma ƙasa baki ɗaya.

“Rayuwar Nana Asma’u na bayar da hujjar tarihi mai ƙarfi cewa ilimin mata ya taɓa daɗewa yana cikin al’ada da darajar addini a Arewa, ba wani abu ne da aka shigo da shi daga waje ba.”

Loading

Tags: Alhaji Sa'ad Abubakar IIIDaular UsmaniyyafimNana Asma'uRahma AbdulmajidSakkwatoSarkin Musulmi
Previous Post

Hajiya Zainab, mahaifiyar jarumin Kannywood Isah A. Isah, ta rasu

Next Post

Mawaƙi a Kannywood, Ahmad Yariman Tiga zai angwance a ranar Juma’a 

Related Posts

Mutuwar aure na ƙaddara ce – Jaruma Khadija Yobe
Labarai

Mutuwar aure na ƙaddara ce – Jaruma Khadija Yobe

August 23, 2026
Aina’u Ade ta raba wa tsofaffin jaruman Kannywood tallafin kuɗi
Labarai

Aina’u Ade ta raba wa tsofaffin jaruman Kannywood tallafin kuɗi

August 23, 2026
Ƙungiyar ‘Triple R Kannywood’ ta ziyarci jarumi Tanimu Akawu a asibiti
Labarai

Ƙungiyar ‘Triple R Kannywood’ ta ziyarci jarumi Tanimu Akawu a asibiti

August 23, 2026
Ƙungiyar Triple R ta ba jarumin Kannywood Mustapha Musty tallafin N500,000
Labarai

Ƙungiyar Triple R ta ba jarumin Kannywood Mustapha Musty tallafin N500,000

August 18, 2026
Yadda na gamu da ibtila’in karaya a ƙafa – Jarumi Ɗan’azumi Kamaye
Labarai

Yadda na gamu da ibtila’in karaya a ƙafa – Jarumi Ɗan’azumi Kamaye

August 14, 2026
Tozali TV zai yi bikin Henna Ball da karrama masu ƙwazo da tallafa wa waɗanda suka tsira daga hare-hare a ranar 31 ga Oktoba
Labarai

Tozali TV zai yi bikin Henna Ball da karrama masu ƙwazo da tallafa wa waɗanda suka tsira daga hare-hare a ranar 31 ga Oktoba

August 8, 2026
Next Post
Mawaƙi a Kannywood, Ahmad Yariman Tiga zai angwance a ranar Juma’a 

Mawaƙi a Kannywood, Ahmad Yariman Tiga zai angwance a ranar Juma'a 

  • Home
  • Game Da Mu
  • Privacy Policy
  • Contact Us

© 2024 Mujallar Fim

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labari
  • Addini
  • Al’adu
  • Iyali
  • Marubuta
  • Mawaƙa
  • Nijeriya
  • Ranar Murna
  • Rayuwa
  • Sharhin Fim
  • Tattaunawa
  • Taurari
  • Tsokaci

© 2024 Mujallar Fim

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In
error: Content is protected !!