• Gida
  • Labarai da Rahotanni
    • Labarai
    • Rahotonni
    • Tattaunawa
  • Sharhi da Tsokaci
    • Sharhin Fim
    • Tsokaci
  • Masu Haskawa
    • Taurarin Fim
    • Marubuta
    • Mawaƙa
  • Addini da Rayuwa
    • Rayuwa
    • Iyalai
    • Al’adu
    • Addini
  • Ranar Murna
Friday, June 6, 2025
  • Login
Kannywood - News, reviews and more  › hausa
  • Gida
  • Labarai da Rahotanni
    • Labarai
    • Rahotonni
    • Tattaunawa
  • Sharhi da Tsokaci
    • Sharhin Fim
    • Tsokaci
  • Masu Haskawa
    • Taurarin Fim
    • Marubuta
    • Mawaƙa
  • Addini da Rayuwa
    • Rayuwa
    • Iyalai
    • Al’adu
    • Addini
  • Ranar Murna
No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai da Rahotanni
    • Labarai
    • Rahotonni
    • Tattaunawa
  • Sharhi da Tsokaci
    • Sharhin Fim
    • Tsokaci
  • Masu Haskawa
    • Taurarin Fim
    • Marubuta
    • Mawaƙa
  • Addini da Rayuwa
    • Rayuwa
    • Iyalai
    • Al’adu
    • Addini
  • Ranar Murna
No Result
View All Result
Kannywood - News, reviews and more  › hausa
No Result
View All Result
  • Gida
  • Labari
  • Addini
  • Al’adu
  • Iyali
  • Marubuta
  • Mawaƙa
  • Nijeriya
  • Ranar Murna
  • Rayuwa
  • Sharhin Fim
  • Tattaunawa
  • Taurari
  • Tsokaci

Haɗa kan Kannywood ne a gaban mu – Gidan Dabino

by DAGA MUKHTAR YAKUBU
December 16, 2022
in Labarai
0
Malam Ado Ahmad Gidan Dabino, MON

Malam Ado Ahmad Gidan Dabino, MON

0
SHARES
0
VIEWS
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsappShare on Telegram

SHUGABAN ƙungiyar ƙwararru ta masu shirya fim ta kara ƙasa (Motion Picture Practitioners Association of Nigeria, MOPPAN), reshen Jihar Kano, Malam Ado Ahmad Gidan Dabino, MON, ya bayyana ƙudirin sa na haɗa kan masu harkar fim da kuma kawo gyara don cigaban masana’antar tasu.

Shugaban ya bayyana haka ne a lokacin tattaunawar sa da mujallar Fim a game da cigaban da ya samar tun daga lokacin da su ka kama shugabancin ƙungiyar tsawon sama da rabin shekara zuwa yanzu.

Shi dai Gidan Dabino, an rantsar da su ne a matsayin shugabannin ƙungiyar a wani taro da aka yi a ɗakin taro na Kannywood TV da ke Tudun Yola, Kano, a ranar Laraba, 27 ga Afrilu, 2022.

Gidan Dabino ya ce: “To, idan ka duba a baya ana ɗan samun kamar zaman doya da manja da wasu ɓangarori, ni kuma abin da na ɗauka idan duk ana masana’anta ɗaya, kowa ɗan’uwan juna ne. Ba za a ce babu wani abu na ƙyashi ko hassada ya shiga tsakani ba, amma dai abin da na ke gani shi ne a taru a yi aiki tare, don mu zama kamar uwa ɗaya ne. Saboda haka, ban zo da niyyar ko na nemi kuɗi ba, na zo ne saboda don an matsa mini na yi shugabancin saboda ana ganin kamar zan iya wani abu, to shi ya sa na zo. Don haka ni na ɗauka kowa uwa ɗaya mu ke, ko wanda ba ma shiri da shi zan iya kiran sa mu zauna mu tattauna a kan wannan masana’antar, ko waɗanda su ke ganin shugabancin ya yi musu ba daidai ba, to a gani na duk ɗaya mu ke.

“Don zan iya tunawa lokacin da aka ba ni shugabancin Ƙungiyar Marubuta ta Ƙasa reshen Jihar Kano, na ga akwai ƙungiyoyin da ba sa shiri da ƙungiyar ANA a lokacin, amma ni na kira su har ya zama mun yi aiki tare, kuma mun yi gamayyar ƙungiyar marubuta wanda mu ka yi faɗan Abubakar Rabo tare da su, wanda idan babu haɗin kai ba za mu yi nasara a faɗan ba.

“Don haka na ke ganin a tunanin da na yi wannan zai taimaki masana’antar Kannywood nan gaba ko da ba mu ne a kai ba, a samu wasu su ɗora daga inda mu ka tsaya.”

Gidan Dabino ya ƙara da cewa abin da ya ke so ya cimma shi ne ya na fatan ‘yan wannan masana’antar su samu ilimi wanda za su samu hanyar sanin wasu abubuwa. Ya ce, “Na biyu, duk da dai ba ma son mu faɗa, amma akwai abubuwan cigaba da mu ke son kawo wa masana’antar a kasuwancin su, ta hanyar samar musu da tallafi, duk da tsawon shugabancin ba shi da yawa, na shekaru biyu ne, kuma a yanzu mun ci kusan sama da rabin shekara. To amma ka san ita harkar ƙungiya sai a hankali, sai dai mu na da fata da kuma buruka da mu ke so mu samar don ganin cigaban masana’antar, don haka kamar yadda na faɗa lokacin da aka zaɓe mu, ba mu ce mun yi alƙawarin za mu yi wa kowa ba, don haka kada a saka mana ido ko a ce kaza. Sai dai in mun yi a gani.

“Don haka mu na fatan Allah ya cika mana burin mu wanda ko da bayan ba ma nan za a ce lallai su wane sun yi wani abu, kuma wannan shi ne fatan mu da mu ke so mu cika in-sha Allah, zuwa lokacin da za mu bayar da shugabancin zuwa ga wasu.”

Loading

Tags: 'yan fimAbubakar RaboAdo Ahmad Gidan DabinoANAhaɗin kaiJihar KanoKannywoodmarubutamasana'antaMOPPANshugaba
Previous Post

Haihuwa: Mansur Makeup da Amina sun samu Afreen

Next Post

Nunu, ‘yar jaruman Kannywood Samira Ahmad da TY Shaban, ta cika shekara 9

Related Posts

An naɗa Shehu Hassan Kano shugaban riƙo na MOPPAN
Labarai

An naɗa Shehu Hassan Kano shugaban riƙo na MOPPAN

June 3, 2025
MOPPAN ta ba gwamnan Kebbi lambar yabo a madadin ‘yan fim
Labarai

MOPPAN ta ba gwamnan Kebbi lambar yabo a madadin ‘yan fim

June 2, 2025
Ƙungiya ta ja kunnen gwamnatin Kano kan dakatar da finafinan Kannywood 22
Labarai

Ƙungiya ta ja kunnen gwamnatin Kano kan dakatar da finafinan Kannywood 22

May 20, 2025
Hukuma ta rufe gidajen gala a Kano har sai bayan Ramadan
Labarai

Gwamnatin Kano ta dakatar da haska finafinan Kannywood 22 a intanet da talbijin 

May 19, 2025
Labarai

Gwamnan Kano ya ɗauki nauyin ‘yan Kannywood 5 zuwa Hajjin bana

April 17, 2025
Sabuwa, matar Ɗanmaraya Jos, ta rasu
Labarai

Sabuwa, matar Ɗanmaraya Jos, ta rasu

March 28, 2025
Next Post
Aisha TY Shaban (Nunu)

Nunu, 'yar jaruman Kannywood Samira Ahmad da TY Shaban, ta cika shekara 9

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

  • Home
  • Game Da Mu
  • Privacy Policy
  • Contact Us

© 2024 Mujallar Fim

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labari
  • Addini
  • Al’adu
  • Iyali
  • Marubuta
  • Mawaƙa
  • Nijeriya
  • Ranar Murna
  • Rayuwa
  • Sharhin Fim
  • Tattaunawa
  • Taurari
  • Tsokaci

© 2024 Mujallar Fim

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In
error: Content is protected !!