• Gida
  • Labarai da Rahotanni
    • Labarai
    • Rahotonni
    • Tattaunawa
  • Sharhi da Tsokaci
    • Sharhin Fim
    • Tsokaci
  • Masu Haskawa
    • Taurarin Fim
    • Marubuta
    • Mawaƙa
  • Addini da Rayuwa
    • Rayuwa
    • Iyalai
    • Al’adu
    • Addini
  • Ranar Murna
Tuesday, August 25, 2026
  • Login
Kannywood - News, reviews and more  › hausa
  • Gida
  • Labarai da Rahotanni
    • Labarai
    • Rahotonni
    • Tattaunawa
  • Sharhi da Tsokaci
    • Sharhin Fim
    • Tsokaci
  • Masu Haskawa
    • Taurarin Fim
    • Marubuta
    • Mawaƙa
  • Addini da Rayuwa
    • Rayuwa
    • Iyalai
    • Al’adu
    • Addini
  • Ranar Murna
No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai da Rahotanni
    • Labarai
    • Rahotonni
    • Tattaunawa
  • Sharhi da Tsokaci
    • Sharhin Fim
    • Tsokaci
  • Masu Haskawa
    • Taurarin Fim
    • Marubuta
    • Mawaƙa
  • Addini da Rayuwa
    • Rayuwa
    • Iyalai
    • Al’adu
    • Addini
  • Ranar Murna
No Result
View All Result
Kannywood - News, reviews and more  › hausa
No Result
View All Result
  • Gida
  • Labari
  • Addini
  • Al’adu
  • Iyali
  • Marubuta
  • Mawaƙa
  • Nijeriya
  • Ranar Murna
  • Rayuwa
  • Sharhin Fim
  • Tattaunawa
  • Taurari
  • Tsokaci

Haska ‘Kalan Dangi’ ya ja ’yan kallo a Kano

by FimMagazine
October 18, 2017
in Labarai
0
'Yan kallo sun yayyabe Aisha Tsamiya

'Yan kallo sun yayyabe Aisha Tsamiya

0
SHARES
0
VIEWS
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsappShare on Telegram

‘Yan kallo sun yayyabe Aisha Tsamiya

CINCIRIDON mutane ne su ka yi tururuwa a gidan sinima na Film House da ke cikin rukunin shagunan Shoprite da ke Ado Bayero Mall, a Kano, wurin shiga kallon fim din ‘Kalan Dangi’ wanda fitacciyar jaruma A’isha Aliyu (‘Tsamiya’) ta dauki nauyin shiryawa. Fauziyya D. Sulaiman ce ta rubuta labarin, yayin da Abubakar Bashir Maishadda ya shirya shi kuma Ali Gumzak ya bada umarni. Wannan dai shi ne fim na biyu da A’isha Tsamiya ta shirya, wato bayan fim din ta na ‘Burin Fatima’, wanda ya fito kasuwa kwanan baya.

Kannywood ta kasance masana’anta wadda ta fi kowace a arewacin Nijeriya samar da ayyukan yi ga matasa cikin kankanen lokaci, amma kasuwanci a cikin ta ya gurgunce a tsawon shekaru sakamakon dogaro da hanya daya ta samar da kudaden shiga (wato kasuwar sayar da fayafayen sidi da dibidi). A lokuta da dama mutane sun yi yunkurin kawo canji a tsarin kasuwancin, amma abin ya ci tura.

Da alama cewa a wannan karon haka za ta cimma ruwa. Dalili kuwa shi ne yadda aka maida haska finafinai a gidajen sinima kafin a sake su a faifan dibidi.

A ranar Juma’a, 1 ga Satumba, 2017, wadda ta zo daidai da ranar Babbar Sallah, aka haska ‘Kalan Dangi’ a sinima. An fara haska fim din da misalin karfe 12:45 na rana, amma a lokacin ba a samu yawaitar mutane ba saboda gabatowar lokacin sallar Juma’a. Sai bayan an taso daga sallar ne, wajen karfe 3, sannan mutane maza da ’yan mata su ka yi tururuwar shiga kallon.

Kafin a fara haskawar, A’isha Tsamiya ta ba masoyan ta dama su dauki hotuna da ita, wanda hakan wani salo ne da aka bullo da shi don a kara jawo mutane zuwa kallon fim. Lokacin nuna finafinan su a sinima bias wannan tsari, Ali Nuhu da Rahama Sadau ma sun yi hakan.

Da yawa daga cikin jarumai da daraktoci sun halarci kallon ‘Kalan Dangi’. Daga cikin su akwai jaruman shirin, wato Ali Nuhu da Fati Washa, da daraktan shirin, Ali Gumzak, sai kuma su Kamal S. Alkali, Aminu Shariff Momoh, Maryam Isah Abubakar (Ceeter), Hafizu Bello, Fauziyya D. Sulaiman, Baballe Hayatu, Mansurah Isah, Hassan Giggs, da sauran su.

An kammala haska fim din karo na biyu da misalin karfe 5:40 na yamma. Fim din ya samu karbuwa saboda irin yadda makallatan sa su ka yi ta Allah-sambarka da tare da ihu yayin da su ke kallon.

Lallai fim din ya samu mahalarta sosai. An yi ittafakin cewa idan aka cire fim din ‘Gwaska’ da aka haska a bara, babu fim din da ya tara ’yan kallo kamar ‘Kalan Dangi’.

Loading

Previous Post

Aisha Tsamiya Za Ta Yi Karatu a Jami’ar NOUN

Next Post

Kannywood ban: Rahama Sadau finally begs Gov. Ganduje, Kano Emir, MOPPAN

Related Posts

Mutuwar aure na ƙaddara ce – Jaruma Khadija Yobe
Labarai

Mutuwar aure na ƙaddara ce – Jaruma Khadija Yobe

August 23, 2026
Aina’u Ade ta raba wa tsofaffin jaruman Kannywood tallafin kuɗi
Labarai

Aina’u Ade ta raba wa tsofaffin jaruman Kannywood tallafin kuɗi

August 23, 2026
Ƙungiyar ‘Triple R Kannywood’ ta ziyarci jarumi Tanimu Akawu a asibiti
Labarai

Ƙungiyar ‘Triple R Kannywood’ ta ziyarci jarumi Tanimu Akawu a asibiti

August 23, 2026
Ƙungiyar Triple R ta ba jarumin Kannywood Mustapha Musty tallafin N500,000
Labarai

Ƙungiyar Triple R ta ba jarumin Kannywood Mustapha Musty tallafin N500,000

August 18, 2026
Yadda na gamu da ibtila’in karaya a ƙafa – Jarumi Ɗan’azumi Kamaye
Labarai

Yadda na gamu da ibtila’in karaya a ƙafa – Jarumi Ɗan’azumi Kamaye

August 14, 2026
Tozali TV zai yi bikin Henna Ball da karrama masu ƙwazo da tallafa wa waɗanda suka tsira daga hare-hare a ranar 31 ga Oktoba
Labarai

Tozali TV zai yi bikin Henna Ball da karrama masu ƙwazo da tallafa wa waɗanda suka tsira daga hare-hare a ranar 31 ga Oktoba

August 8, 2026
Next Post
Rahama Sadau

Kannywood ban: Rahama Sadau finally begs Gov. Ganduje, Kano Emir, MOPPAN

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

  • Home
  • Game Da Mu
  • Privacy Policy
  • Contact Us

© 2024 Mujallar Fim

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labari
  • Addini
  • Al’adu
  • Iyali
  • Marubuta
  • Mawaƙa
  • Nijeriya
  • Ranar Murna
  • Rayuwa
  • Sharhin Fim
  • Tattaunawa
  • Taurari
  • Tsokaci

© 2024 Mujallar Fim

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In
error: Content is protected !!