• Gida
  • Labarai da Rahotanni
    • Labarai
    • Rahotonni
    • Tattaunawa
  • Sharhi da Tsokaci
    • Sharhin Fim
    • Tsokaci
  • Masu Haskawa
    • Taurarin Fim
    • Marubuta
    • Mawaƙa
  • Addini da Rayuwa
    • Rayuwa
    • Iyalai
    • Al’adu
    • Addini
  • Ranar Murna
Monday, June 16, 2025
  • Login
Kannywood - News, reviews and more  › hausa
  • Gida
  • Labarai da Rahotanni
    • Labarai
    • Rahotonni
    • Tattaunawa
  • Sharhi da Tsokaci
    • Sharhin Fim
    • Tsokaci
  • Masu Haskawa
    • Taurarin Fim
    • Marubuta
    • Mawaƙa
  • Addini da Rayuwa
    • Rayuwa
    • Iyalai
    • Al’adu
    • Addini
  • Ranar Murna
No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai da Rahotanni
    • Labarai
    • Rahotonni
    • Tattaunawa
  • Sharhi da Tsokaci
    • Sharhin Fim
    • Tsokaci
  • Masu Haskawa
    • Taurarin Fim
    • Marubuta
    • Mawaƙa
  • Addini da Rayuwa
    • Rayuwa
    • Iyalai
    • Al’adu
    • Addini
  • Ranar Murna
No Result
View All Result
Kannywood - News, reviews and more  › hausa
No Result
View All Result
  • Gida
  • Labari
  • Addini
  • Al’adu
  • Iyali
  • Marubuta
  • Mawaƙa
  • Nijeriya
  • Ranar Murna
  • Rayuwa
  • Sharhin Fim
  • Tattaunawa
  • Taurari
  • Tsokaci

Haska ‘Kalan Dangi’ ya ja ’yan kallo a Kano

by FimMagazine
October 18, 2017
in Labarai
0
'Yan kallo sun yayyabe Aisha Tsamiya

'Yan kallo sun yayyabe Aisha Tsamiya

0
SHARES
0
VIEWS
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsappShare on Telegram

‘Yan kallo sun yayyabe Aisha Tsamiya

CINCIRIDON mutane ne su ka yi tururuwa a gidan sinima na Film House da ke cikin rukunin shagunan Shoprite da ke Ado Bayero Mall, a Kano, wurin shiga kallon fim din ‘Kalan Dangi’ wanda fitacciyar jaruma A’isha Aliyu (‘Tsamiya’) ta dauki nauyin shiryawa. Fauziyya D. Sulaiman ce ta rubuta labarin, yayin da Abubakar Bashir Maishadda ya shirya shi kuma Ali Gumzak ya bada umarni. Wannan dai shi ne fim na biyu da A’isha Tsamiya ta shirya, wato bayan fim din ta na ‘Burin Fatima’, wanda ya fito kasuwa kwanan baya.

Kannywood ta kasance masana’anta wadda ta fi kowace a arewacin Nijeriya samar da ayyukan yi ga matasa cikin kankanen lokaci, amma kasuwanci a cikin ta ya gurgunce a tsawon shekaru sakamakon dogaro da hanya daya ta samar da kudaden shiga (wato kasuwar sayar da fayafayen sidi da dibidi). A lokuta da dama mutane sun yi yunkurin kawo canji a tsarin kasuwancin, amma abin ya ci tura.

Da alama cewa a wannan karon haka za ta cimma ruwa. Dalili kuwa shi ne yadda aka maida haska finafinai a gidajen sinima kafin a sake su a faifan dibidi.

A ranar Juma’a, 1 ga Satumba, 2017, wadda ta zo daidai da ranar Babbar Sallah, aka haska ‘Kalan Dangi’ a sinima. An fara haska fim din da misalin karfe 12:45 na rana, amma a lokacin ba a samu yawaitar mutane ba saboda gabatowar lokacin sallar Juma’a. Sai bayan an taso daga sallar ne, wajen karfe 3, sannan mutane maza da ’yan mata su ka yi tururuwar shiga kallon.

Kafin a fara haskawar, A’isha Tsamiya ta ba masoyan ta dama su dauki hotuna da ita, wanda hakan wani salo ne da aka bullo da shi don a kara jawo mutane zuwa kallon fim. Lokacin nuna finafinan su a sinima bias wannan tsari, Ali Nuhu da Rahama Sadau ma sun yi hakan.

Da yawa daga cikin jarumai da daraktoci sun halarci kallon ‘Kalan Dangi’. Daga cikin su akwai jaruman shirin, wato Ali Nuhu da Fati Washa, da daraktan shirin, Ali Gumzak, sai kuma su Kamal S. Alkali, Aminu Shariff Momoh, Maryam Isah Abubakar (Ceeter), Hafizu Bello, Fauziyya D. Sulaiman, Baballe Hayatu, Mansurah Isah, Hassan Giggs, da sauran su.

An kammala haska fim din karo na biyu da misalin karfe 5:40 na yamma. Fim din ya samu karbuwa saboda irin yadda makallatan sa su ka yi ta Allah-sambarka da tare da ihu yayin da su ke kallon.

Lallai fim din ya samu mahalarta sosai. An yi ittafakin cewa idan aka cire fim din ‘Gwaska’ da aka haska a bara, babu fim din da ya tara ’yan kallo kamar ‘Kalan Dangi’.

Loading

Previous Post

Aisha Tsamiya Za Ta Yi Karatu a Jami’ar NOUN

Next Post

Kannywood ban: Rahama Sadau finally begs Gov. Ganduje, Kano Emir, MOPPAN

Related Posts

Wani maigida na ya ce wahalar banza nake yi a kan Yerima Shettima, inji Hussaini Danko
Labarai

Wani maigida na ya ce wahalar banza nake yi a kan Yerima Shettima, inji Hussaini Danko

June 13, 2025
Jarumin Kannywood, Abdul M. Shareef zai auri jaruma Maryam Malika
Labarai

Jarumin Kannywood, Abdul M. Shareef zai auri jaruma Maryam Malika

June 12, 2025
Hukumar Tace Finafinai ta Kano ta yaba wa ɗakunan taruka bisa bin doka da oda lokacin bukukuwan Sallah
Labarai

Hukumar Tace Finafinai ta Kano ta yaba wa ɗakunan taruka bisa bin doka da oda lokacin bukukuwan Sallah

June 12, 2025
Rahama Sadau ta raba barka da Sallah ga ‘yan fim na Kaduna
Labarai

Rahama Sadau ta raba barka da Sallah ga ‘yan fim na Kaduna

June 11, 2025
‘Aure tsakanin jaruman Kannywood, Mansurah da Momoh’: Yadda lamarin yake
Labarai

‘Aure tsakanin jaruman Kannywood, Mansurah da Momoh’: Yadda lamarin yake

June 11, 2025
An naɗa Shehu Hassan Kano shugaban riƙo na MOPPAN
Labarai

An naɗa Shehu Hassan Kano shugaban riƙo na MOPPAN

June 3, 2025
Next Post
Rahama Sadau

Kannywood ban: Rahama Sadau finally begs Gov. Ganduje, Kano Emir, MOPPAN

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

  • Home
  • Game Da Mu
  • Privacy Policy
  • Contact Us

© 2024 Mujallar Fim

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labari
  • Addini
  • Al’adu
  • Iyali
  • Marubuta
  • Mawaƙa
  • Nijeriya
  • Ranar Murna
  • Rayuwa
  • Sharhin Fim
  • Tattaunawa
  • Taurari
  • Tsokaci

© 2024 Mujallar Fim

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In
error: Content is protected !!