KITSO da kwarkwata ya sanya haɗaɗɗiyar ƙungiyar masu shirya finafinan Hausa ta Nijeriya (MOPPAN) ta ƙasa reshen Jihar Kano yin kwaskwarima ga shugabancin kwamitin riƙon zaɓen ta na Kano.
Shugaban ƙungiyar na 3 na ƙasa, Alhaji Adamu Musa Jahun, shi ne ya bayyana haka a yayin wata tattaunawa da ya yi da mujallar Fim kan dalilan da ya jawo sauyin shugabancin kwamitin riƙo na ƙungiyar a yau Litinin, 6 ga Yuli, 2021.
Dambarwar na zuwa ne a daidai lokacin da wasu daga cikin ‘ya’yan ƙungiyar ke zargin tsohon jagoran da shirin siyasantar da tafiyar ƙungiyar, wanda hakan ya saɓa da manufofin ƙungiyar.
Da ya ke bayani kan dalilan da su ka sa ƙungiya ta ɗauki wannan mataki, Jahun ya ce, ”Waɗanda aka ba su ragamar gudanar da shirye-shiryen zaɓe, sai ya zama a cikin tafiya da ta yi tafiya a wancan lokaci aka fahimci cewa akwai waɗanda su ke da buƙatar su ma su tsaya neman kujerar shugabancin ɓangaren MOPPAN na Jihar Kano, a tsari idan zai zama cewa akwai wanda ya ya ke a matsayin jagora kuma a lokaci guda zai tsaya a matsayin neman takarar kujerar shugabanci dole zai zamo akwai gyara a cikin hidimar.
“Ba zai yiwu ka na shugabantar kwamitin zaɓe kuma a lokaci guda kai ma ka na ɗan takara ba. Dole ne ka ajiye kujerar ka ta shugabancin kwamitin zaɓe ko kuma ka ajiye kujerar ka ta hukumar zaɓe, ka dawo ka shiga takara.”
Jahun ya ƙara da cewa, “Shugabancin ƙungiya na ƙasa ya lura da irin ce-ce-ku-ce da aka samu tsakanin mambobin ƙungiyar, wanda idan aka bar hakan ya ci gaba da tafiya a matsayin mu na shuwagabannin ƙungiya na ƙasa, to za a yi kitso ne da ƙwarƙwata. Shi ya sa mu ka yi wa abin togaciya.

“Haka ya sa ƙungiya ta ƙara naɗa wasu shuwagabannin riƙo da za su jagoranci wannan kwamitin na zaɓe domin su ci gaba da jagoranci har zuwa lokacin da za a gudanar da zaɓe.”
Kazalika ya ce, “Kasancewar Kano ita ce kan gaba wajen gudanar da wannan harkokin namu, don duk wanda ya ke harkokin fim a ƙasar nan in dai a Arewa ya ke to dole ya na tutuya ne da Jihar Kano, duk inda aka je aka zo nan dai Kano ɗin shi ne cibiya, a nan kuma ake harhaɗa komai da komai, ko da a ce ana buƙatar abubuwa daga nan Kano dai ake ɗaukar miƙati. Shi ya sa mu ka ga cewa ya za a yi mu gyara yadda wannan zaɓe na Kano zai zamto ya tafi cikin nasara ba tare da an samu tasgaro ko kuma ce-ce-ku-ce ba duk da hidindumun zaɓe ba ka isa ka ce ba za a samu irin wannan ba domin a yayin da ka ke ƙoƙarin tsara abubuwa su ta fi daidai, a yayin ne kuma wasu su ke ganin su ba a musu daidai ba.
“Kuma dalilin da ya sa mu ka yi duba ga mutanen da su ke jajirtattu, waɗanda su ka zamto sun hidimtu kuma su na kan hidima da wannan masana’antar tamu, mu ka ga ya dace mu ba su ragamar gudanar da jagorancin wannan zaɓe domin za su iya.”
A ƙarshe, ya bayyana cewa nan ba da jimawa ba uwar ƙungiya ta ƙasa za ta miƙa wa sababbin shugabannin riƙon ƙwarya jadawalin yadda za su gudanar da ayyukan su domin gudanar da zaɓen su cikin nasara.
Sababbin shugabannin riƙon ƙwarya da za su jagoranci kwamitin sun haɗa da Nasir B. Muhammad a matsayin shugaba da kuma mataimakin sa Ishaq Sidi Ishaq.
![]()







