• Gida
  • Labarai da Rahotanni
    • Labarai
    • Rahotonni
    • Tattaunawa
  • Sharhi da Tsokaci
    • Sharhin Fim
    • Tsokaci
  • Masu Haskawa
    • Taurarin Fim
    • Marubuta
    • Mawaƙa
  • Addini da Rayuwa
    • Rayuwa
    • Iyalai
    • Al’adu
    • Addini
  • Ranar Murna
Sunday, June 15, 2025
  • Login
Kannywood - News, reviews and more  › hausa
  • Gida
  • Labarai da Rahotanni
    • Labarai
    • Rahotonni
    • Tattaunawa
  • Sharhi da Tsokaci
    • Sharhin Fim
    • Tsokaci
  • Masu Haskawa
    • Taurarin Fim
    • Marubuta
    • Mawaƙa
  • Addini da Rayuwa
    • Rayuwa
    • Iyalai
    • Al’adu
    • Addini
  • Ranar Murna
No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai da Rahotanni
    • Labarai
    • Rahotonni
    • Tattaunawa
  • Sharhi da Tsokaci
    • Sharhin Fim
    • Tsokaci
  • Masu Haskawa
    • Taurarin Fim
    • Marubuta
    • Mawaƙa
  • Addini da Rayuwa
    • Rayuwa
    • Iyalai
    • Al’adu
    • Addini
  • Ranar Murna
No Result
View All Result
Kannywood - News, reviews and more  › hausa
No Result
View All Result
  • Gida
  • Labari
  • Addini
  • Al’adu
  • Iyali
  • Marubuta
  • Mawaƙa
  • Nijeriya
  • Ranar Murna
  • Rayuwa
  • Sharhin Fim
  • Tattaunawa
  • Taurari
  • Tsokaci

Mai ƙarar Rahama Sadau ya kafa wa ‘yansanda sharuɗɗan ba ta beli

by DAGA IRO MAMMAN
November 8, 2020
in Labarai
0
Rahama Sadau ta sha nanata cewa ita ba ta ci zarafin Manzo ba

Rahama Sadau ta sha nanata cewa ita ba ta ci zarafin Manzo ba

0
SHARES
0
VIEWS
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsappShare on Telegram
MUTUMIN nan da ya rubuta takardar koke kan Rahama Sadau ya gindaya wa ‘yansanda sharuɗɗan da za su bi kafin su ba ta beli.
 
Idan kun tuna, mutumin, wani mazaunin Abuja mai suna Malam Lawal Muhammad Gusau, ya kai koke ga Sufeto-Janar na ‘Yansandan Nijeriya a kan fitacciyar jarumar ta Kannywood da Nollywood, shi kuma ya bada umarnin a kama ta.
 
A yau ne dai ake sa ran Rahama za ta bayyana a ofishin Kwamishinan ‘Yansanda na Jihar Kaduna, Umar Muri, don amsa gayyatar da ya yi mata bisa umarnin na Sufeto-Janar.
 
Wata majiya mai tushe ta faɗa wa mujallar Fim cewa kwamishinan ya ɗaga wa jarumar ƙafa ne a kan zuwan ta ofishin sa jiya kamar yadda aka tsara, ya ce ta je a yau Lahadi.
 
Rahama da ƙannen ta mata su uku da mahaifiyar ta sun iso Kaduna a makare daga Abuja jiya bayan sun fasa tafiyar da su ka ƙudiri aniyar yi zuwa Dubai saboda umarnin na Sufeto-Janar.
 
‘Yansanda na binciken ta ne bisa zargin da Lawal Gusau ya rubuta a kan cewar wai ta aikata saɓo a kan Manzon Allah (SAW).
 
Tuni dai Rahama ta sha nuna wa jama’a cewa ba ita ce ta ci zarafin Annabi (SAW) ba, wani mutum ne daban ya aikata hakan a ƙarƙashin wasu hotuna da ta tura a Tuwita. 
 
Haka kuma tuni ta goge hotunan tare da bada haƙuri ga ɗaukacin Musulmi kan abin da ya faru.
 
Sai dai a yayin da ta ke shirin zuwa hedikwatar ‘yansanda ta Kaduna, Lawal Gusau ya gindaya wa ‘yansandan sharuɗɗan bada belin ta a wata sanarwa ga manema labarai da ya saki a daren jiya.
 
Mujallar Fim ta fassaro sharuɗɗan kamar haka:
 
Na ɗaya, tilas ne lauyan Rahama Sadau ya kasance Musulmi. Dalilin sa shi ne lauya Musulmi ne kaɗai ya san yadda ake shari’a a kotun Shari’ar Musulunci inda ake aiki da Alƙur’ani da Hadisan Annabi (SAW), ba kundin Tsarin Mulkin Nijeriya ba.
 
Lawal Gusau ya gindaya sharuɗɗan beli masu zafi
 
Na biyu, tilas ne aikin ‘yansanda ya tsaya ga aikin su na ɗaukar Rahama su na kai ta kotun Shari’ar Musulunci kaɗai bayan sun yi binciken sirri kan al’amarin.
 
Na uku, Malam Lawal ya bada sunayen malaman da ya ke so su zauna su yi wa Rahama alƙalanci kan saɓon da ya ke zargin ta da aikatawa. 
 
Malaman  da ya zaɓa, waɗanda dukkan su daga ɓangaren Izala ne, su ne: Sheikh Dakta Ahmed Mahmoud Gumi daga Kaduna; Sheikh Ahmed BUK daga Kano; Sheikh Kabir Haruna Gombe daga Gombe; Sheikh Nura Khalil (Digital) daga Abuja da kuma Ministan Sadarwa Sheikh Ali Isa Pantami.
 
Sharaɗi na huɗu da ya bayar kuma shi ne kada wani lauya daga Kaduna ko ma Arewa baki ɗaya ya tsoma baki cikin wannan magana ta Rahama Sadau.
 
A ƙarshe, Malam Lawal Muhammad Gusau ya yi kira ga jama’a da su kwantar da hankalin su domin, kamar yadda ya ce, za a yanke wa Rahama hukuncin da ya dace da ita.
 
Wata majiya ta ce lauyan Rahama Sadau ne zai take mata sawu zuwa ganin Kwamishina Umar Muri a safiyar yau.

Loading

Previous Post

Yadda Sufeto-Janar ya umarci kwamishina ya kama Rahama Sadau

Next Post

Menene laifin Rahama Sadau?

Related Posts

Wani maigida na ya ce wahalar banza nake yi a kan Yerima Shettima, inji Hussaini Danko
Labarai

Wani maigida na ya ce wahalar banza nake yi a kan Yerima Shettima, inji Hussaini Danko

June 13, 2025
Jarumin Kannywood, Abdul M. Shareef zai auri jaruma Maryam Malika
Labarai

Jarumin Kannywood, Abdul M. Shareef zai auri jaruma Maryam Malika

June 12, 2025
Hukumar Tace Finafinai ta Kano ta yaba wa ɗakunan taruka bisa bin doka da oda lokacin bukukuwan Sallah
Labarai

Hukumar Tace Finafinai ta Kano ta yaba wa ɗakunan taruka bisa bin doka da oda lokacin bukukuwan Sallah

June 12, 2025
Rahama Sadau ta raba barka da Sallah ga ‘yan fim na Kaduna
Labarai

Rahama Sadau ta raba barka da Sallah ga ‘yan fim na Kaduna

June 11, 2025
‘Aure tsakanin jaruman Kannywood, Mansurah da Momoh’: Yadda lamarin yake
Labarai

‘Aure tsakanin jaruman Kannywood, Mansurah da Momoh’: Yadda lamarin yake

June 11, 2025
An naɗa Shehu Hassan Kano shugaban riƙo na MOPPAN
Labarai

An naɗa Shehu Hassan Kano shugaban riƙo na MOPPAN

June 3, 2025
Next Post
Rahama Sadau

Menene laifin Rahama Sadau?

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

  • Home
  • Game Da Mu
  • Privacy Policy
  • Contact Us

© 2024 Mujallar Fim

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labari
  • Addini
  • Al’adu
  • Iyali
  • Marubuta
  • Mawaƙa
  • Nijeriya
  • Ranar Murna
  • Rayuwa
  • Sharhin Fim
  • Tattaunawa
  • Taurari
  • Tsokaci

© 2024 Mujallar Fim

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In
error: Content is protected !!