• Gida
  • Labarai da Rahotanni
    • Labarai
    • Rahotonni
    • Tattaunawa
  • Sharhi da Tsokaci
    • Sharhin Fim
    • Tsokaci
  • Masu Haskawa
    • Taurarin Fim
    • Marubuta
    • Mawaƙa
  • Addini da Rayuwa
    • Rayuwa
    • Iyalai
    • Al’adu
    • Addini
  • Ranar Murna
Sunday, June 15, 2025
  • Login
Kannywood - News, reviews and more  › hausa
  • Gida
  • Labarai da Rahotanni
    • Labarai
    • Rahotonni
    • Tattaunawa
  • Sharhi da Tsokaci
    • Sharhin Fim
    • Tsokaci
  • Masu Haskawa
    • Taurarin Fim
    • Marubuta
    • Mawaƙa
  • Addini da Rayuwa
    • Rayuwa
    • Iyalai
    • Al’adu
    • Addini
  • Ranar Murna
No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai da Rahotanni
    • Labarai
    • Rahotonni
    • Tattaunawa
  • Sharhi da Tsokaci
    • Sharhin Fim
    • Tsokaci
  • Masu Haskawa
    • Taurarin Fim
    • Marubuta
    • Mawaƙa
  • Addini da Rayuwa
    • Rayuwa
    • Iyalai
    • Al’adu
    • Addini
  • Ranar Murna
No Result
View All Result
Kannywood - News, reviews and more  › hausa
No Result
View All Result
  • Gida
  • Labari
  • Addini
  • Al’adu
  • Iyali
  • Marubuta
  • Mawaƙa
  • Nijeriya
  • Ranar Murna
  • Rayuwa
  • Sharhin Fim
  • Tattaunawa
  • Taurari
  • Tsokaci

Maikano da Mado sun yi tsokaci kan zumunci tsakanin ‘yan fim

by DAGA ABBA MUHAMMAD
May 8, 2023
in Labarai
0
Daga hagu: Abdullahi Maikano da Nura Mado

Daga hagu: Abdullahi Maikano da Nura Mado

0
SHARES
0
VIEWS
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsappShare on Telegram

TSOHON shugaban Haɗaɗɗiyar Ƙungiyar Masu Shirya Finafinai ta Nijeriya (MOPPAN), Alhaji Abdullahi Maikano Usman, ya yi tsokaci game da hirar furodusa Abubakar Anka kan batun farfaɗo da zumunci a tsakanin ‘yan fim.

Maikano ya yi tsokacin ne a daidai lokacin da ya ga wasu daga cikin ‘yan Kannywood a cikin wani guruf mai suna ‘MOPPAN Associates’ su na muhawara kan hirar ta Anka.

Kafin Maikano ya ce wani abu, sai jarumi Nura Mado ya fara magana bayan tura hirar da wakilin mujallar Fim ya yi a cikin guruf ɗin, inda ya ce, “Ai ko yanzu ana zumunci, musamman ma in mutum ya na da kuɗi ko wata dama.”

Duk da cewa lallai ya karanta labarin ba, ya dai ga kanun ne ya yi magana. Sai wakilin mu ya ba shi amsa da cewa, “Ba irin wannan zumuncin ya ke magana ba.”

Sai ya ba da amsa da cewa, “Kowane irin zumunci ya ke magana, yanzu dai kuɗi ko wata dama su ake wa zumunci, zumuncin da an yi shi da, kuma ba zai taɓa dawowa ba sai dai a kamanta.”

Nan wani Ambasada Abdul Ismael ya yi dariya, sai Nuran ya ce masa, “Ah to, ai gaskiya ne Amb, zumuncin nan fa na industiri na da ɗin da mu aka yi, haka yanzun ma ga mu ana yin na yanzun ma da mu, ka ga kuwa ai mu na da ta cewa a kai.”

Sai Ambasada ya ce masa, “A gaskiya ni na yarda da zancen ka, saboda daga ranar da ka gani a jarida Buhari ya yi mun ‘S.A. Petroleum Down Stream’ kullum sai kira na ka ke yi mu na zumunci da ko ba ka yin hakan hhhhh.” 

Mado ya amsa masa da cewa, “Ah to ai ko ina ne not only our industry, but kawai dai mu na mu ya fi worst of capitalism.”

Ya yi dariya, ya ce masa “Sure?”

Nura ya ce, “Sosai, ka sani, na sani sun sani, mun sani.”

Wannan muhawarar ce ta sa Abdullahi Maikano shi ma ya tofa albarkacin bakin sa, inda ya ce, “Salamu alaikum ‘yan’uwa. Na leƙo wannan zaure mai matuƙar muhimmanci sai na ga ana tattaunawa kan zumunci, muhimmancin sa da kuma yadda alamarin ya ke a masana’antar mu a da can baya da kuma yadda abin ya ke a halin yanzu.”

Maikano ya ci gaba da cewa, “Ni kai na a matsayi na na ɗan wannan masana’anta, na kasance a lokuta da dama ina jimamin yadda zumunci ya yi ƙaranci tsakanin mu musamman idan aka kwatanta da yadda abin ya ke a da can baya.

“Na san lokutan da ɗan Kano zai yi takakkiya zuwa Kaduna don taya ɗan’uwan sa aiki ko wata murna a Kaduna. 

“Ina da masaniyar yadda ake cika mota daga Kaduna domin ba da gudunmawa ko taimako ko murna ko jimami ga wani ko wasu a Kano ko Zariya ko Sokoto, kai har ma da Jos da sauran wurare.

“Wani abin mamaki ma shi ne wani daga cikin waɗanda ake kai zumuncin da shi bai ma san wanda za a je wajen na sa ba. Zallar ƙauna ce kawai.”

Ya ƙara da cewa, “Dalilai biyu ne na ke ganin su ka haifar da haka. Na farko ƙaunar juna da son cigaban juna, sai kuma na biyu, yi domin Allah. Ina sane da lokacin da Hajiya Balaraba Ramat da Hajiya Umma su ka yi wo aiken turame ga wani biki da aka yi a Kaduna. Duk wani mai tsohuwar mujallar Fim ya zaƙulo su ya duba ya ga yadda ake tururuwar zuwa bukukuwan juna da sanya alhairi da taya juna murna. Ni ina ganin kamar abin ya ja baya. Ban sani ba ko ni kaɗai na ke kallon abin ta haka.”

Maikano ya kawo mafita, inda ya ce, “Son juna da taimakon juna da yi wa ɗan’uwa fatan alhairi na ɗaya daga cikin abubuwan da ke janyo nasara. Shin ka san yi wa ɗan’uwa addu’a ba tare da ya san ka yi masa addu’a ba wata hanya ce ta tsira da karin arziki? 

“Mu so juna mu taimakawa juna. Sannan ka yi wa kowa fatan alhairi na ɗaya daga cikin mabuɗan alhairi.”

Nura Mado ya ce, “Wannan gaskiya ne ran ka ya daɗe, Allah ya saka da alkhairi ya ba mu ikon gyara zumuncin mu.”

Loading

Tags: Abdullahi Maikano UsmanAbubakar AnkaKannywoodMOPPANNura Madozumunci
Previous Post

Rasuwar Kawu Mala na shirin ‘Daɗin Kowa’ ta girgiza jama’a

Next Post

Nagari Na Kowa: Tasirin Muhammad Nami A Hukumar Tara Kuɗaɗen Haraji Ta Ƙasa (FIRS)

Related Posts

Wani maigida na ya ce wahalar banza nake yi a kan Yerima Shettima, inji Hussaini Danko
Labarai

Wani maigida na ya ce wahalar banza nake yi a kan Yerima Shettima, inji Hussaini Danko

June 13, 2025
Jarumin Kannywood, Abdul M. Shareef zai auri jaruma Maryam Malika
Labarai

Jarumin Kannywood, Abdul M. Shareef zai auri jaruma Maryam Malika

June 12, 2025
Hukumar Tace Finafinai ta Kano ta yaba wa ɗakunan taruka bisa bin doka da oda lokacin bukukuwan Sallah
Labarai

Hukumar Tace Finafinai ta Kano ta yaba wa ɗakunan taruka bisa bin doka da oda lokacin bukukuwan Sallah

June 12, 2025
Rahama Sadau ta raba barka da Sallah ga ‘yan fim na Kaduna
Labarai

Rahama Sadau ta raba barka da Sallah ga ‘yan fim na Kaduna

June 11, 2025
‘Aure tsakanin jaruman Kannywood, Mansurah da Momoh’: Yadda lamarin yake
Labarai

‘Aure tsakanin jaruman Kannywood, Mansurah da Momoh’: Yadda lamarin yake

June 11, 2025
An naɗa Shehu Hassan Kano shugaban riƙo na MOPPAN
Labarai

An naɗa Shehu Hassan Kano shugaban riƙo na MOPPAN

June 3, 2025
Next Post
Muhammad M. Nami

Nagari Na Kowa: Tasirin Muhammad Nami A Hukumar Tara Kuɗaɗen Haraji Ta Ƙasa (FIRS)

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

  • Home
  • Game Da Mu
  • Privacy Policy
  • Contact Us

© 2024 Mujallar Fim

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labari
  • Addini
  • Al’adu
  • Iyali
  • Marubuta
  • Mawaƙa
  • Nijeriya
  • Ranar Murna
  • Rayuwa
  • Sharhin Fim
  • Tattaunawa
  • Taurari
  • Tsokaci

© 2024 Mujallar Fim

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In
error: Content is protected !!