MAIMUNATU Kabir Ɗan’auta, tsohuwar matar shahararren mawaƙi kuma jarumin barkwanci a Kannywood, Ado Isah Gwanja, ta yi aure a karo na uku jiya Juma’a.
Wata ƙwaƙƙwarar majiya ta tabbatar wa da mujallar Fim labarin auren, wanda aka ɗaura a asirce a Kano a daidai lokacin da hankalin jama’a ya raja’a kan tataɓurzar da ake yi kan sarautar Sarkin Kano.
Majiyar ba ta faɗa mana sunan angon ba domin Maimunatu ta ce ba za ta bayyana shi ba har sai lokacin da za ta yi bikin tarewa. Maimunatu na kiran kan ta da “Mrs. A” a cikin ‘yan kwanakin nan a soshiyal midiya.
Wato kenan an ɗaura auren babu tarewa sai nan da wani lokaci.
Mai ba mu labarin ya ce: “Maimuna ta burge ni domin ba ta tsaya ɓata lokaci ba ta kuma yin aure.”
Ita dai Maimunatu, auren ta da Gwanja ya mutu da saki uku ne a cikin 2021.
Sun haifi ‘ya guda ɗaya mai suna Asiya (Balaraba), wadda aka haifa a ranar Asabar, 17 ga Agusta, 2019.
Mujallar Fim ta ruwaito cewa wannan auren da aka ɗaura jiya shi ne na uku da Maimunatu ta yi, domin kuwa ta taɓa yin auren kisan wuta a Abuja bayan rabuwar su da Gwanja.
Ta yi matuƙar son ta koma wa uban ‘yar ta, wato Ado Gwanja, shi kuma sai ya ƙi. An ce ya faɗa wa wasu makusantan sa cewa shi da Maimunatu ba za su taɓa komawa aure ba.
Don haka ne ma aka ɗaura masa aure da matar sa ta yanzu, wato Maryam Zubair Muhammad Paki, a ranar 21 ga Yuli, 2023 a Kano.
“Ganin ba zai maida ta ba ne ya saka Maimunatu ta yanke shawarar bari dai ta kama dahir,” a cewar majiyar mujallar Fim.
Maimunatu dai ta yi fice da sunan @munat_danautah a soshiyal midiya inda a kai a kai ta kan wallafa hotuna da bidiyoyin ta masu bayyana kyakkyawar surar ta.
![]()







