• Gida
  • Labarai da Rahotanni
    • Labarai
    • Rahotonni
    • Tattaunawa
  • Sharhi da Tsokaci
    • Sharhin Fim
    • Tsokaci
  • Masu Haskawa
    • Taurarin Fim
    • Marubuta
    • Mawaƙa
  • Addini da Rayuwa
    • Rayuwa
    • Iyalai
    • Al’adu
    • Addini
  • Ranar Murna
Thursday, May 14, 2026
  • Login
Kannywood - News, reviews and more  › hausa
  • Gida
  • Labarai da Rahotanni
    • Labarai
    • Rahotonni
    • Tattaunawa
  • Sharhi da Tsokaci
    • Sharhin Fim
    • Tsokaci
  • Masu Haskawa
    • Taurarin Fim
    • Marubuta
    • Mawaƙa
  • Addini da Rayuwa
    • Rayuwa
    • Iyalai
    • Al’adu
    • Addini
  • Ranar Murna
No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai da Rahotanni
    • Labarai
    • Rahotonni
    • Tattaunawa
  • Sharhi da Tsokaci
    • Sharhin Fim
    • Tsokaci
  • Masu Haskawa
    • Taurarin Fim
    • Marubuta
    • Mawaƙa
  • Addini da Rayuwa
    • Rayuwa
    • Iyalai
    • Al’adu
    • Addini
  • Ranar Murna
No Result
View All Result
Kannywood - News, reviews and more  › hausa
No Result
View All Result
  • Gida
  • Labari
  • Addini
  • Al’adu
  • Iyali
  • Marubuta
  • Mawaƙa
  • Nijeriya
  • Ranar Murna
  • Rayuwa
  • Sharhin Fim
  • Tattaunawa
  • Taurari
  • Tsokaci

Manazarta sun yi kwamba a KASU kan rubutun Hausa

by DAGA ABBA MUMAMMAD
November 15, 2019
in Labarai
0
Wani sashe na mahalarta taron

Wani sashe na mahalarta taron

0
SHARES
0
VIEWS
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsappShare on Telegram

KAMAR yadda ya saba yi a duk shekara, a bana ma Sashen Nazarin Harsunan Nijeriya da Ilimin Harsuna na Jami’ar Jihar Kaduna (KASU) ya shirya taron ƙara wa juna sani. Taron na bana an shirya shi ne kan abin da ya shafi harshen Hausa. 

 An buɗe taron a yau tare da taken “Daidaitacciyar Hausa da Ƙa’idojin Rubutu’.  

Wannan shi ne karo na 5 da sashen ya shirya taron, wanda Farfesa Ibrahim Muhammad Malumfashi ke jagoranta. 

Taron, wanda aka sa za a gudanar da shi daga ranar Alhamis, 14 ga Nuwamba zuwa Lahadi, 17 ga Nuwamba, 2019, an fara gudanar da taron ne a yau Juma’a, 15 ga Nuwamba, 2019 a ɗakin karatu na jami’ar da ke Titin Tafawa Ɓalewa, cikin garin Kaduna. 

Farfesa Imam Abdulkarim, Farfesa Aliyu Idris Funtua, da Farfesa Abdullahi Ashafa a taron

 Dakta Mu’az na Sashen Larabci na KASU ne ya buɗe taron da addu’a da misalin ƙarfe 10:51 na safe. Daga nan sai Malumfashi ya gabatar da jawabin maraba inda kuma ya gabatar da manyan baƙi. 

 Ya bayyana cewa daga cikin manyan manazartan da aka gayyata har da gogaggen masanin nan a fannin nazarin harshen Hausa mazaunin Ingila, Farfesa Graham Furniss, to amma bai samu damar halarta ba, ya dai aiko da saƙon bada haƙuri.

 Daga nan aka buɗe fage, manazarta su ka fantsama cikin gabatar da ƙasidu, waɗanda su na da dama, kuma masu nuni da yadda ake rubutu da Hausa da yadda ƙa’idojin rubutu su ke. 

 An tashi daga taron da misalin ƙarfe 1:20 na rana da nufin cewa gobe za a ɗora daga inda aka tsaya.

 Manyan malamai da manazartan Hausa da ‘yan siyasa da ɗalibai sun halarci zaman na yau. 

Farfesa Bello Sa’id (a dama) da Farfesa Ibrahim Malumfashi

Manyan sun haɗa da Farfesa Abdullahi Ashafa, wakilin mataimakin shugaban jami’ar ta KASU, Dakta Aliyu Isa Sulaiman, Farfesa Muhammad Dauda Bagari Azare, Farfesa Hamisu Miko Yakasai, Farfesa Bello Sa’id, Farfesa Mukhtar Yusuf,  Farfesa Imam Abdulkarim, Alh. Ado Ahmad Gidan Dabino (MON), Dakta Aliyu Idris Funtua, Farfesa Halliru Ahmad Amfani, da Honarabul Ibrahim Sulaiman Dabo. 

Loading

Previous Post

Gwamnatin Kano ta ɗau nauyin bikin finafinai na BON

Next Post

Ana yi wa ƙa’idojin rubuta Hausa karan tsaye a soshiyal midiya, inji Farfesa Aliyu Funtua

Related Posts

Rasuwar dattijon Kannywood, Nura Shareef, ta girgiza ‘yan fim
Labarai

Rasuwar dattijon Kannywood, Nura Shareef, ta girgiza ‘yan fim

February 22, 2026
Daraktar fim ta ƙi karɓar awad saboda kisan gillar da Isra’ila take yi a Gaza
Labarai

Daraktar fim ta ƙi karɓar awad saboda kisan gillar da Isra’ila take yi a Gaza

February 21, 2026
Fitaccen furodusa Kunle Afolayan ya yi haɗin gwiwa da Jamhuriyar Benin kan shirya finafinai
Labarai

Fitaccen furodusa Kunle Afolayan ya yi haɗin gwiwa da Jamhuriyar Benin kan shirya finafinai

February 19, 2026
An naɗa Farfesa Tengya matsayin sabon shugaban Cibiyar Koyon Finafinai ta Ƙasa
Labarai

An naɗa Farfesa Tengya matsayin sabon shugaban Cibiyar Koyon Finafinai ta Ƙasa

February 15, 2026
Alƙali ya ci Samha Inuwa tara ko ta je kurkuku wata 6
Labarai

Alƙali ya ci Samha Inuwa tara ko ta je kurkuku wata 6

February 13, 2026
Hukumar EFCC ta kama jarumar Kannywood, Samha Inuwa, saboda goge majina da takardun naira
Labarai

Hukumar EFCC ta kama jarumar Kannywood, Samha Inuwa, saboda goge majina da takardun naira

February 3, 2026
Next Post
Farfesa Aliyu Idris Funtua na gabatar da jawabin sa a taron KASU

Ana yi wa ƙa'idojin rubuta Hausa karan tsaye a soshiyal midiya, inji Farfesa Aliyu Funtua

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

  • Home
  • Game Da Mu
  • Privacy Policy
  • Contact Us

© 2024 Mujallar Fim

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labari
  • Addini
  • Al’adu
  • Iyali
  • Marubuta
  • Mawaƙa
  • Nijeriya
  • Ranar Murna
  • Rayuwa
  • Sharhin Fim
  • Tattaunawa
  • Taurari
  • Tsokaci

© 2024 Mujallar Fim

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In
error: Content is protected !!