MAWAƘIYAR yabon Annabi, Maimuna Ibrahim, ta yi saukar haddar Alƙur’ani mai girma.
An yi bikin saukar ne a ranar Asabar, 30 ga Nuwamba, 2024.
Maimuna, wadda aka fi sani da laƙabin Ummi Burdatu, ta bayyana wa mujallar Fim farin cikin ta a game da bikin saukar.
Ta ce, “Biki uku ne ba zan manta da su ba a rayuwa ta. Farko NCE graduation. Na biyu Islamiyya graduation na uku Tahfiz graduation (hadda), duk a ƙarƙashin jagorancin mahaifiya ta.
“Oh Mama! Ke kaɗai nake ji da gani a wannan duniyar; ke ce rayuwa ta. Allah ya ba ni ikon faranta miki, mahaifiya ta.”

Ummi Burdatu tana ɗaya daga cikin mata masu waƙoƙin yabon Annabi Muhammadu (S.A.W.) kuma tana daga cikin ‘yan Ƙungiyar Sha’irai ta Burdattunaby, inda a nan ta samu laƙabin ta.
![]()







