• Gida
  • Labarai da Rahotanni
    • Labarai
    • Rahotonni
    • Tattaunawa
  • Sharhi da Tsokaci
    • Sharhin Fim
    • Tsokaci
  • Masu Haskawa
    • Taurarin Fim
    • Marubuta
    • Mawaƙa
  • Addini da Rayuwa
    • Rayuwa
    • Iyalai
    • Al’adu
    • Addini
  • Ranar Murna
Monday, April 6, 2026
  • Login
Kannywood - News, reviews and more  › hausa
  • Gida
  • Labarai da Rahotanni
    • Labarai
    • Rahotonni
    • Tattaunawa
  • Sharhi da Tsokaci
    • Sharhin Fim
    • Tsokaci
  • Masu Haskawa
    • Taurarin Fim
    • Marubuta
    • Mawaƙa
  • Addini da Rayuwa
    • Rayuwa
    • Iyalai
    • Al’adu
    • Addini
  • Ranar Murna
No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai da Rahotanni
    • Labarai
    • Rahotonni
    • Tattaunawa
  • Sharhi da Tsokaci
    • Sharhin Fim
    • Tsokaci
  • Masu Haskawa
    • Taurarin Fim
    • Marubuta
    • Mawaƙa
  • Addini da Rayuwa
    • Rayuwa
    • Iyalai
    • Al’adu
    • Addini
  • Ranar Murna
No Result
View All Result
Kannywood - News, reviews and more  › hausa
No Result
View All Result
  • Gida
  • Labari
  • Addini
  • Al’adu
  • Iyali
  • Marubuta
  • Mawaƙa
  • Nijeriya
  • Ranar Murna
  • Rayuwa
  • Sharhin Fim
  • Tattaunawa
  • Taurari
  • Tsokaci

MOPPAN ta kafa kwamitin zaɓe da masu ba da shawara

by ABBA MUHAMMAD
September 9, 2024
in Labarai
0
MOPPAN ta kafa kwamitin zaɓe da masu ba da shawara

Habibu Barde Mohammed, Shugaban Riƙo na MOPPAN

0
SHARES
0
VIEWS
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsappShare on Telegram

ƘUNGIYAR Masu Shirya Fina-finai ta Nijeriya (MOPPAN), ta gudanar da taro a Abuja, inda ta ƙaddamar da kwamitin zaɓe da masu bada shawara gabanin gagarumin zaɓen sababbin shugabannin ƙungiyar na ƙasa.

Kakakin Ƙungiyar na Ƙasa, Malam Al-Amin Ciroma, ne ya sanar da kafa kwamitin a wata takardar manema labarai da ya fitar a daren jiya Lahadi, wanda mujallar Fim ta samu kwafi.

Takardar ta ce:

Shugabannin Ƙungiyar Masu Shirya Fina-finai ta Nijeriya (MOPPAN), sun gudanar da muhimmin taro a ranar Asabar, 7 ga Satumba, 2024 a Abuja, wanda Shugaban Ƙungiyar na Ƙasa, Alhaji Habibu Barde Mohammed, ya jagoranta.

A yayin taron, an tattauna muhimman batutuwan da su ka shafi makomar ƙungiyar, inda aka yi shawarwari kamar haka:

Kafa kwamitin zaɓe, wanda an kafa kwamitin zaɓe mai mutane 13 da za su kula da babban taron ƙungiyar ta MOPPAN da zaɓukan da za a yi a ranar Asabar ta farko a watan Janairun 2025, a wurin da za a bayyana a nan gaba kaɗan, domin bai wa kwamitin zaɓen cikakken wakilci a cikin masana’antar da ƙananan kwamitoci.

Bayan tattaunawa mai tsawo, kwamitin gudanarwa ta MOPPAN ta amince da cewa Alhaji Bala Mu’azu Kufaina daga cikin shugabannin na ƙasa na yanzu zai zama Shugaban Kwamitin; Nasiru S. Gwangwazo, Mataimakin Shugaban MOPPAN, reshen Abuja, zai zama Sakataren Kwamitin.

Wasu daga cikin mambobin kwamitin sun haɗa da Alhaji Abdul Amart, Malam Umar UK, Hajiya Umma Shehu, da Hajiya Hadiza Muhammad (Hadizan Saima), waɗanda dukkan su wakilan Kannywood ne.

Sauran mambobin kwamitin sun haɗa da Alhaji Ado Ahmed Gidan Dabino (MON), Shugaban Ƙungiyar MOPPAN, reshen Jihar Kano; Alhaji Hamisu Jibrin Goma, Shugaban MOPPAN, reshen Jihar Kaduna, dukkan su masu wakiltar Arewa maso Yamma.

Alhaji Umar Rabi, Shugaban MOPPAN na Jihar Filato da Alhaji Ado Mohammed, Shugaban MOPPAN na Jihar Neja kuma, za su wakilci shiyyar Arewa ta Tsakiya.

Shugaban MOPPAN, reshen Jihar Yobe, Malam Mohammed Khalifa da Shugaban MOPPAN, reshen Jihar Bauchi, Malam Babaye Bauchi su ne za su wakilci shiyyar Arewa maso Gabas a kwamitin.

Wannan daidai ne. Abin lura a nan shi ne, kafin a amince da waɗanda aka zaɓa, uku daga cikin shugabannin sai sun shaidawa kwamitin cewa ba su da niyyar tsayawa takara a kowane muƙami a zaɓen ƙasa mai zuwa.

Alhaji Habibu Barde Mohammed, Shugaban Ƙungiyar ta Ƙasa, Alhaji Salisu Mu’azu, Sakataren Janar na Ƙungiyar na Ƙasa, da Alhaji Bala Mu’azu Kufaina, ma’ajin ƙungiyar ta ƙasa.

Na biyu: Naɗin zaɓe da masu bada shawara.

Shugaban Ƙungiyar MOPPAN na Ƙasa, Alhaji Habibu Barde Mohammed, ya amince da naɗa mambobin kwamitin zaɓe, Malam Ahmed Alkanawi da Mohammed Gumel a matsayin masu ba da shawara kan dabaru ga kwamitocin zaɓe da na taro a ƙarƙashin sakatariyar, domin tabbatar da shirye-shirye da haɗin kai, naɗe-naɗe na babban taro da zaɓuka masu zuwa bisa la’akari da irin ƙwarewar da su ke da shi a irin waɗannan ayyuka tare da manyan ayyuka a gaba.

Sakataren kwamitin zaɓe zai gayyace su don halartar taro ko tarukan kwamitoci inda ake buƙatar gudummawar su kowane lokaci.

Na uku: Zaɓukan Jihohi. Hukumar zaɓen MOPPAN ta umurci dukkan sassan jihohin da har yanzu ba su gudanar da zaɓukan su, wanda lokaci ya wuce da su gudanar ƙarshen watan Nuwamba, 2024.

Jihohin sun haɗa da Gombe, Katsina, Kebbi, Kogi, Kwara, da Zamfara.

Duk jihar da ta ƙi bin umarnin, ba za ta cancanci kawo wakilai don shiga zaɓen ƙasa na MOPPAN da za a yi a ranar Asabar ta farko ta Janairu 2025 ba, komai daidai yake.

Na huɗu: Mambobin MOPPAN na ƙarƙashin jagorancin Alhaji Habibu Barde Mohammed, ya jajirce wajen ganin an gudanar da sahihin zaɓe na gaskiya da adalci, don haka ya na kira ga ɗaukacin ma’aikatan masana’antar da na kwamitin amintattu da su goyi bayan ƙoƙarin membobi na ƙasa da sabon kwamitin zaɓen da aka kafa, don tabbatar da fitar da gwani a lokacin babban taro da zaɓuka masu zuwa.

Don haka ana kira ga ɗaukacin ‘yan masana’antar da su fito su tsaya takara a kan duk wani muƙami da ya yi daidai da fannin ku da gogewar ku a harkar daga kowace shiyya a ƙasar nan.

Na biyar: A halin yanzu, don ba da lokaci mai yawa ga ‘yan kwamitin zaɓe su fara shirya kan su ta guruf ɗin ‘WhatsApp’ da sakataren tsare-tsare zai ƙirƙira da kuma MOPPAN ta gudanar da sauran sassan shirye-shiryen ta na dabarun da ke gabanta kafin zaɓe.

Mu na sa ido a ranar Alhamis 24 ga Oktoba don gudanar da taron mambobi na haɗin gwiwa tare da sabbin mambobin kwamitin zaɓe na ƙasa, don ƙaddamar da su tare da miƙa musu sharuɗɗan su da sauran ƙa’idojin da su ka dace don ba su damar ci-gaba da ayyukan su ba tare da wani cikas ba.

Loading

Tags: Al-Amin CiromaHabibu Barde MuhammadKannywoodMOPPANzaɓe
Previous Post

Mawaƙi Aminu Nomiis Gee ya samu ƙaruwar ‘ya mace

Next Post

Minista Idris ya jajanta wa al’ummar Neja da iyalan mutum 59 da suka mutu sakamakon fashewar tankar mai

Related Posts

Rasuwar dattijon Kannywood, Nura Shareef, ta girgiza ‘yan fim
Labarai

Rasuwar dattijon Kannywood, Nura Shareef, ta girgiza ‘yan fim

February 22, 2026
Daraktar fim ta ƙi karɓar awad saboda kisan gillar da Isra’ila take yi a Gaza
Labarai

Daraktar fim ta ƙi karɓar awad saboda kisan gillar da Isra’ila take yi a Gaza

February 21, 2026
Fitaccen furodusa Kunle Afolayan ya yi haɗin gwiwa da Jamhuriyar Benin kan shirya finafinai
Labarai

Fitaccen furodusa Kunle Afolayan ya yi haɗin gwiwa da Jamhuriyar Benin kan shirya finafinai

February 19, 2026
An naɗa Farfesa Tengya matsayin sabon shugaban Cibiyar Koyon Finafinai ta Ƙasa
Labarai

An naɗa Farfesa Tengya matsayin sabon shugaban Cibiyar Koyon Finafinai ta Ƙasa

February 15, 2026
Alƙali ya ci Samha Inuwa tara ko ta je kurkuku wata 6
Labarai

Alƙali ya ci Samha Inuwa tara ko ta je kurkuku wata 6

February 13, 2026
Hukumar EFCC ta kama jarumar Kannywood, Samha Inuwa, saboda goge majina da takardun naira
Labarai

Hukumar EFCC ta kama jarumar Kannywood, Samha Inuwa, saboda goge majina da takardun naira

February 3, 2026
Next Post
Gwamnati ba ta musanya sunan Titin Murtala Muhammed da na Soyinka ba, inji Minista

Minista Idris ya jajanta wa al'ummar Neja da iyalan mutum 59 da suka mutu sakamakon fashewar tankar mai

  • Home
  • Game Da Mu
  • Privacy Policy
  • Contact Us

© 2024 Mujallar Fim

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labari
  • Addini
  • Al’adu
  • Iyali
  • Marubuta
  • Mawaƙa
  • Nijeriya
  • Ranar Murna
  • Rayuwa
  • Sharhin Fim
  • Tattaunawa
  • Taurari
  • Tsokaci

© 2024 Mujallar Fim

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In
error: Content is protected !!