SANANNEN mawaƙin nan da ke Kaduna, Sagir Ɗanyaro (Baban Kausar), ya bayyana fitaccen mawaƙin siyasa El-Mu’az Muhammad Birniwa da cewa shi mutum ne da ya ke iya yi wa mutane hidima da duk abin da ya ke da shi ba tare da ya damu ba, kuma “mai irin wannan hali duk abin da ya yi ba zai zama abin mamaki ba.”
Baban Kausar ya faɗi haka ne a hirar da ya yi da mujallar Fim sakamakon kyautar dalleliyar mota ƙirar Ford (samfurin Focus) da aminin nasa ya yi masa a yau.
Baban Kausar da kan sa ya sanar wa da duniya wannan abin arzikin da aka yi masa a shafin sa na Instagram, inda ya rubuta: “Alhamdu lillah! Layi ya zo kan mu, El-Mu’az Muhammad Birniwa ya gwangwaje ni da mota ƙirar Ford Focus.”
Ya biyo sanarwar da roƙon cewa, “Allah ya saka masa da gidan Aljanna, Allah ya ƙarfafa gaban sa da bayan sa, ya ƙara buɗe ƙofofin arziki, ya tsare masa mutuncin sa don mutuncin Annabi Muhammadu (S.A.W.).”
Da wakilin mujallar Fim ya tambayi Baban Kausar abin da zai ce game da wannan kyauta ta El-Mu’az ne ya ce, “To, da farko dai ina miƙa godiya ga Allah maɗaukakin Sarki a bisa doron ikon sa wannan kyautar ta wanzu.
“Sai kuma in ƙara jeranta salatuka ga fiyayyen halitta, Annabin farko da ƙarshe (s.a.w.), wanda bisa gwadaben soyayyar sa mu ka haɗu a matsuguni guda, mu ke rayuwa tare a matsayin aminai kuma abokan sana’a.”
Ya ci gaba da cewa, “Duk mutumin da ka ce ya kawo maka na kusa da El-Mu’az Birniwa a Kaduna, ina da yaƙinin sai ya harsaso ni a cikin mutane ukun farko. A haka mu ke rayuwa tsawon lokaci, har wasu na tunanin ko mu ‘yan’uwa ne na jini saboda kyakkyawar alaƙa da ke tsakanin mu.
“Allah maɗaukakin Sarki ya fifita shi a kan mu, ko in ce ya ɗaukaka shi sama da mu. Hakan bai sa ya wulaƙanta mu ba; a haka dai mu ke ta rayuwa tare.
“Haka ya sa ban yi mamaki ba da ya ce ya saya min mota saboda na san zai iya abin da ya fi hakan. Ko yanzu ai mu uku ya saya wa motar.
“Shi mutum ne da ya ke iya yi wa mutane hidima da duk abin da ya ke da shi ba tare da ya damu ba. Mai irin wannan hali duk abin da ya yi ba zai zama abin mamaki ba.
“Fata na Allah ya yi masa jagora a cikin lamarin sa, ya kare gaban sa da bayan sa. Allah ya sa Aljanna makoma gare shi da mu baki ɗaya.
“Allah ya jiƙan magabatan mu, ya sa su na kyakkyawan matsayi, alfarmar Annabi Muhammadu (s.a.w.).”
Ɗimbin mutane sun taya Baban Kausar murnar wannan kyauta da aka yi masa.
Shi da El-Mu’az dai duk mazauna garin Kaduna ne.
![]()






