• Gida
  • Labarai da Rahotanni
    • Labarai
    • Rahotonni
    • Tattaunawa
  • Sharhi da Tsokaci
    • Sharhin Fim
    • Tsokaci
  • Masu Haskawa
    • Taurarin Fim
    • Marubuta
    • Mawaƙa
  • Addini da Rayuwa
    • Rayuwa
    • Iyalai
    • Al’adu
    • Addini
  • Ranar Murna
Wednesday, August 26, 2026
  • Login
Kannywood - News, reviews and more  › hausa
  • Gida
  • Labarai da Rahotanni
    • Labarai
    • Rahotonni
    • Tattaunawa
  • Sharhi da Tsokaci
    • Sharhin Fim
    • Tsokaci
  • Masu Haskawa
    • Taurarin Fim
    • Marubuta
    • Mawaƙa
  • Addini da Rayuwa
    • Rayuwa
    • Iyalai
    • Al’adu
    • Addini
  • Ranar Murna
No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai da Rahotanni
    • Labarai
    • Rahotonni
    • Tattaunawa
  • Sharhi da Tsokaci
    • Sharhin Fim
    • Tsokaci
  • Masu Haskawa
    • Taurarin Fim
    • Marubuta
    • Mawaƙa
  • Addini da Rayuwa
    • Rayuwa
    • Iyalai
    • Al’adu
    • Addini
  • Ranar Murna
No Result
View All Result
Kannywood - News, reviews and more  › hausa
No Result
View All Result
  • Gida
  • Labari
  • Addini
  • Al’adu
  • Iyali
  • Marubuta
  • Mawaƙa
  • Nijeriya
  • Ranar Murna
  • Rayuwa
  • Sharhin Fim
  • Tattaunawa
  • Taurari
  • Tsokaci

Tilas Mu Ceci Kan Mu Da Kan Mu, Inji Wasila

by DAGA MUKHTAR YAKUBU A KANO
October 11, 2017
in Labarai
0
Tilas Mu Ceci Kan Mu Da Kan Mu, Inji Wasila
0
SHARES
0
VIEWS
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsappShare on Telegram

SHUGABAR kungiyar ’yan fim mata wadanda su ka yi aure, Hajiya Wasila Isma’il, ta bayyana cewa tilas ne matan industiri das u ka yi aure su kula da kan su ta fuskar tarbiyya, su taimaki kan su da kan su, domin kuwa duk abin da ’yan bayan su su ka yi, to zai iya shafar su.

Ta fadi haka ne a wani kwarya-kwaryan taro da kungiyar tasu ta gudanar a Kano kwanan nan.

Sun yi taron ne kamar yadda su ka saba yi a duk shekara, wanda su ka hada shi da shagalin bikin Babbar Sallah. Hakan ya bai wa fitattun jarumai mata da su ka dade ba su ga juna ba damar halartar taron.

Matan sun yi taron a ranar Litinin, 4 ga Satumba, 2017 a wani wajen shakatawa mai suna Green Park da ke Titin Ahmadu Bello a cikin garin Kano.

Tun da farko da ta ke jawabi a wajen, Wasila Isma’il ta bayyana matukar farin cikin ta a game da yadda mata ’yan fim su ka amsa gayyatar su da aka yi. A cewar ta, duk da cewar an yi taro har sau uku a baya, amma babu wani taro da jama’a su ka taru kamar wannan din.

“Haka alama ce da ke nuna manufar mu ta kafa wannan kungiya mai amfani ce, shi ya sa mata su ka amsa gayyatar da mu ka yi masu,” inji ta.

Ta ci gaba da cewa, “A farkon wannan kungiya, mun kafa ta ne don mata ’yan fim da su ka yi aure, ta yadda za mu rinka taimaka wa junan mu, to amma daga baya sai mu ka duba, akwai mata ’yan fim da su ka yi aure kuma auren nasu ya mutu, kuma su na bukatar taimako, don haka ne mu ka buda kungiyar ta zama ta matan aure da su ke gidan mijin su da kuma wadanda auren su ya mutu.

“Don haka ne a wannan taron za ku ga akwai mata da yawa da auren su ya mutu, kuma sun halarci wannan taron. Mun amince mu hadu mu yi tafiya da su, ta haka ne za mu san wadanda su ke da matsaloli kuma mu san hanyar da za mu bi mu tallafa masu, domin mun gano akwai da dama da aka sake su aka bar masu kula da yara.

“Wasu kuma mazajen su ne su ka rasu su ka bar su da yara, don haka akwai bukatar a tallafa masu.

“A yanzu a halin da ake ciki, mu ’yan fim mu na bukatar mu hada kan mu domin mu magance matsalar da ta ke damun matan da su ke cikin harkar fim saboda yadda ake kallon ’yan fim din, domin kada mu rika ganin mun yi aure mun bar harkar, to duk abin da na bayan mu su ka yi to zai shafe mu.

“Kamar maganar da ake yi na cewar ’yan fim ba sa zaman aure, to ni ga ni shekara ta goma sha biyar da aure ina tare da miji na, don haka maganar ’yan fim ba sa zaman aure ba gaskiya ba ne. Mutuwar aure idan ta zo a ko’ina ma ana yi, ba sai ’yan fim ba.”

Daga karshe, Wasila, wadda matar darakta Al-Amin Ciroma ce, ta yi kira ga mata ’yan fim da su ci gaba da kiyaye mutuncin su a duk inda su ka samu kan su.

Ita ma da ta ke jawabi, tsohuwar jaruma Saima Mohammed Raga ta kalubalanci wadanda su ke cewa ’yan fim ’yan iska ne, ta ce wannan ba gaskiya ba ne, domin idan mutum ya so lalacewa ba sai ya shigo harkar fim ba.

“Don haka mu sana’a mu ke yi, ba iskanci ba. Duk da ba za mu ce dukkan mu mutanen kirki ba ne, amma bai kamata a rinka yi mana kudin goro ba,” inji ta.

An dai yi jawabai da dama a wajen, sannan kuma an ware lokacin nishadantar da mahalarta taron inda aka tuna baya wajen saka tsofaffin wakokin finafinan jaruman da su ka hau wakar su na bin ta. Fati Mohammed ita ta hau wakar ‘Sangaya’, Rasheeda Adamu Abdullahi ta hau wakar fim din ‘Sa’a’, kuma duk da yake yanzu ta yi nauyi amma hakan bai hana ta yin rawa da juyi ba; Mansura Isah an saka mata wakar bikin su da Sani Danja.

A karshen taron, an cimma matsayar cewa za a samar da tallafi ga iyalan ’yan fim da su ka rasu, irin su Jamila Haruna, Hajiya Amina Garba (Mama Dumba), da sauran su.

Loading

Previous Post

Yadda Rasheeda da Abida su ka kusa dambacewa

Next Post

Aisha Tsamiya Za Ta Yi Karatu a Jami’ar NOUN

Related Posts

Mutuwar aure na ƙaddara ce – Jaruma Khadija Yobe
Labarai

Mutuwar aure na ƙaddara ce – Jaruma Khadija Yobe

August 23, 2026
Aina’u Ade ta raba wa tsofaffin jaruman Kannywood tallafin kuɗi
Labarai

Aina’u Ade ta raba wa tsofaffin jaruman Kannywood tallafin kuɗi

August 23, 2026
Ƙungiyar ‘Triple R Kannywood’ ta ziyarci jarumi Tanimu Akawu a asibiti
Labarai

Ƙungiyar ‘Triple R Kannywood’ ta ziyarci jarumi Tanimu Akawu a asibiti

August 23, 2026
Ƙungiyar Triple R ta ba jarumin Kannywood Mustapha Musty tallafin N500,000
Labarai

Ƙungiyar Triple R ta ba jarumin Kannywood Mustapha Musty tallafin N500,000

August 18, 2026
Yadda na gamu da ibtila’in karaya a ƙafa – Jarumi Ɗan’azumi Kamaye
Labarai

Yadda na gamu da ibtila’in karaya a ƙafa – Jarumi Ɗan’azumi Kamaye

August 14, 2026
Tozali TV zai yi bikin Henna Ball da karrama masu ƙwazo da tallafa wa waɗanda suka tsira daga hare-hare a ranar 31 ga Oktoba
Labarai

Tozali TV zai yi bikin Henna Ball da karrama masu ƙwazo da tallafa wa waɗanda suka tsira daga hare-hare a ranar 31 ga Oktoba

August 8, 2026
Next Post
Aisha Tsamiya

Aisha Tsamiya Za Ta Yi Karatu a Jami'ar NOUN

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

  • Home
  • Game Da Mu
  • Privacy Policy
  • Contact Us

© 2024 Mujallar Fim

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labari
  • Addini
  • Al’adu
  • Iyali
  • Marubuta
  • Mawaƙa
  • Nijeriya
  • Ranar Murna
  • Rayuwa
  • Sharhin Fim
  • Tattaunawa
  • Taurari
  • Tsokaci

© 2024 Mujallar Fim

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In
error: Content is protected !!