• Gida
  • Labarai da Rahotanni
    • Labarai
    • Rahotonni
    • Tattaunawa
  • Sharhi da Tsokaci
    • Sharhin Fim
    • Tsokaci
  • Masu Haskawa
    • Taurarin Fim
    • Marubuta
    • Mawaƙa
  • Addini da Rayuwa
    • Rayuwa
    • Iyalai
    • Al’adu
    • Addini
  • Ranar Murna
Wednesday, May 6, 2026
  • Login
Kannywood - News, reviews and more  › hausa
  • Gida
  • Labarai da Rahotanni
    • Labarai
    • Rahotonni
    • Tattaunawa
  • Sharhi da Tsokaci
    • Sharhin Fim
    • Tsokaci
  • Masu Haskawa
    • Taurarin Fim
    • Marubuta
    • Mawaƙa
  • Addini da Rayuwa
    • Rayuwa
    • Iyalai
    • Al’adu
    • Addini
  • Ranar Murna
No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai da Rahotanni
    • Labarai
    • Rahotonni
    • Tattaunawa
  • Sharhi da Tsokaci
    • Sharhin Fim
    • Tsokaci
  • Masu Haskawa
    • Taurarin Fim
    • Marubuta
    • Mawaƙa
  • Addini da Rayuwa
    • Rayuwa
    • Iyalai
    • Al’adu
    • Addini
  • Ranar Murna
No Result
View All Result
Kannywood - News, reviews and more  › hausa
No Result
View All Result
  • Gida
  • Labari
  • Addini
  • Al’adu
  • Iyali
  • Marubuta
  • Mawaƙa
  • Nijeriya
  • Ranar Murna
  • Rayuwa
  • Sharhin Fim
  • Tattaunawa
  • Taurari
  • Tsokaci

‘Yan Kannywood sun kai ziyarar ta’aziyyar rasuwar Hanifa Abubakar

by DAGA MUHAMMAD LAWAN RANO
January 27, 2022
in Labarai
0
Umar Gombe, edita Suleiman Abubakar da jaruman Kannywood mata a lokacin ziyarar

Umar Gombe, edita Suleiman Abubakar da jaruman Kannywood mata a lokacin ziyarar

0
SHARES
0
VIEWS
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsappShare on Telegram

‘YAN fim ɗin Hausa su na daga cikin ɗimbin mutanen da su ke yin tururuwa zuwa wajen kai ziyarar ta’aziyya ga iyayen ƙaramar yarinyar nan ‘yar shekara 5 wadda malamin makarantar su ya kashe, wato Hanifa Abubakar.

Haɗaɗɗiyar ƙungiyar masu shirya finafinai ta Nijeriya (MOPPAN) reshen Jihar Kano, ita ce ta wakilci ‘yan fim ɗin wajen kai ziyarar a yau Alhamis a ƙarƙashin jagorancin shugaban ta na riƙo, fitaccen jarumi Umar Mohammed Gombe. 

A makon da ya gabata ne dai aka gano gawar Hanifa bayan wanda ake zargin ya sace ta tare da kashe ta ta hanyar ba ta shinkafar ɓera ta sha, sannan ya daddatsa ta, kuma ya binne ta a harabar makarantar su ta Noble Kids da ke unguwar Dakata a birnin Kano.

Da ya ke bayyana alhini kan lamarin ga mujallar Fim, Umar Gombe ya nuna matuƙar alhini game da ɗanyen aikin da malamin makarantar ya aikata, ya ce, ”Ban taɓa ganin tashin hankali irin wannan lamari da ya faru kan wannan baiwar Allah ba, a ce yau malami wanda ake iya ba shi amanar rai shi zai yi irin wannan aika-aika, ba ƙaramin tashin hankali ba ne kuma a ƙasa ƙasar Musulunci, Musulunci da aka san shi da jinƙai da aiwatar da abu daidai.

“To ba abin da za mu ce sai dai Allah ya tsare mu daga mummunar ƙaddara.”

Mata ‘yan fim a gidan su marigayiya Hanifa Abubakar

Mata ‘yan fim a gidan su marigayiya Hanifa Abubakar

Shugaban ƙungiyar ta MOPPAN ya sha alwashin tsayawa tsayin daka wajen ganin an ƙwato wa yarinyar haƙƙin ta.

Tawagar ‘yan Kannywood da su ka je ta’aziyyar tare da Umar Gombe sun haɗa da Sulaiman Abubukar, Saima Mohammed, Asma’u Sani, Aisha Yola da Asma’u Muhammad.

Shi dai wanda ake zargi da kisan kan, mai suna Abdulmalik Tanko, an gurfanar da shi a gaban kotun majistire da ke Gidan Murtala, a ranar Litinin da ta gabata, 24 ga Janairu, 2022.

Loading

Tags: Abdulmalik TankoAsma'u Sani.Hanifa AbubakarKanoMOPPANNoble Kids SchoolSaima MohammedUmar Gombe
Previous Post

Babu uzirin kasa cimma nasara a zaɓen Abuja, inji shugaban INEC

Next Post

Ba ja: Ahmad Sarari ya sake zama shugaban MOPPAN na ƙasa

Related Posts

Rasuwar dattijon Kannywood, Nura Shareef, ta girgiza ‘yan fim
Labarai

Rasuwar dattijon Kannywood, Nura Shareef, ta girgiza ‘yan fim

February 22, 2026
Daraktar fim ta ƙi karɓar awad saboda kisan gillar da Isra’ila take yi a Gaza
Labarai

Daraktar fim ta ƙi karɓar awad saboda kisan gillar da Isra’ila take yi a Gaza

February 21, 2026
Fitaccen furodusa Kunle Afolayan ya yi haɗin gwiwa da Jamhuriyar Benin kan shirya finafinai
Labarai

Fitaccen furodusa Kunle Afolayan ya yi haɗin gwiwa da Jamhuriyar Benin kan shirya finafinai

February 19, 2026
An naɗa Farfesa Tengya matsayin sabon shugaban Cibiyar Koyon Finafinai ta Ƙasa
Labarai

An naɗa Farfesa Tengya matsayin sabon shugaban Cibiyar Koyon Finafinai ta Ƙasa

February 15, 2026
Alƙali ya ci Samha Inuwa tara ko ta je kurkuku wata 6
Labarai

Alƙali ya ci Samha Inuwa tara ko ta je kurkuku wata 6

February 13, 2026
Hukumar EFCC ta kama jarumar Kannywood, Samha Inuwa, saboda goge majina da takardun naira
Labarai

Hukumar EFCC ta kama jarumar Kannywood, Samha Inuwa, saboda goge majina da takardun naira

February 3, 2026
Next Post
Sabon shugaba, Dakta Ahmad Sarari, ya na gabatar da jawabi a babban taron MOPPAN na ƙasa jiya a Kano

Ba ja: Ahmad Sarari ya sake zama shugaban MOPPAN na ƙasa

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

  • Home
  • Game Da Mu
  • Privacy Policy
  • Contact Us

© 2024 Mujallar Fim

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labari
  • Addini
  • Al’adu
  • Iyali
  • Marubuta
  • Mawaƙa
  • Nijeriya
  • Ranar Murna
  • Rayuwa
  • Sharhin Fim
  • Tattaunawa
  • Taurari
  • Tsokaci

© 2024 Mujallar Fim

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In
error: Content is protected !!