SHUGABAN Haɗaɗɗiyar Ƙungiyar Masu Shirya Finafinai ta Nijeriya (MOPPAN), reshen Jihar Kano, Malam Ado Ahmad Gidan Dabino, ya bayyana cewa ƙungiyar ta kafa wani kwamiti da zai samar da gudunmawar kuɗi domin tallafa wa ‘yan fim waɗanda su ka yi asara a tarzomar bayan zaɓen gwamnan jihar domin rage masu raɗaɗin abin da ya same su.
Ƙungiyar dai a karan kan ta ta bayar da gudunmawar N100,000, yayin da shugabannin ta kowanne ya bayar da N10,000, wanda a nan take su ka samar da jimillar kuɗi N220,000.
A lokacin da mujallar Fim ta nemi jin ta bakin sa, Gidan Dabino ya ce: “Su waɗannan ‘yan’uwan mu ne kuma abokan sana’ar mu ne, don haka duk wani abu da ya same su, to ya shafe mu. Don haka mu ka samar da wani kwamiti da zai haɗa ɗan abin da ya samu na tallafi domin a ba su don su ɗan samu sassaucin raɗaɗin abin da ya faru na mummunar asarar da su ka yi.
“Don haka kamar yadda wasu ƙungiyoyi na cikin Kannywood su ka yi, mu ma mun yi wannan yunƙurin, mu na sa ran a cikin wannan satin mu haɗa abin da mu ka samu mu gabatar masu da shi domin su ɗan samu abin da za su ɗan yi buƙatun azumi, wanda a yanzu kowa ya san halin da ake ciki, kuma sun samu kan su a yanayin ibtila’i, don ba ƙaramar asara aka yi ba wanda bayan an kwashe kayayyakin su wasu kuma an ƙone wajen nasu ne ƙurmus, don haka mu ka ƙudiri aniyar tallafa masu, wanda har yanzu ƙofa a buɗe ta ke, mu na neman gudunmawar kowa da kowa.”
Ƙone kayan dai da fashe-fashe ya shafi ofisoshi huɗu ne – na Dauda Rarara, Baban Chinedu, Ahmad M. Sadiq, da Rabi’u The King wanda shi ne aka ƙone shi ƙurmus bayan an kwashe kayayyakin da ke ciki.
Irin wannan abu da ke biyo bayan fitar da sakamakon zaɓe ga ‘yan fim a Kano ba sabon abu ba ne. A cikin 2011 da aka bayyana Shugaban Ƙasa Jonathan a matsayin wanda ya ci zaɓe, an farfasa wajen Nura Hussaini da Baba Ƙarami, sannan aka yi ta farautar Sani Danja za a kashe shi saboda ɗan PDP ne a lokacin, wanda har sai da ta kai shi ga barin Kano ya tare a Abuja.