SHUGABAN riƙo na Ƙungiyar Masu Shirya Finafinai ta Nijeriya (MOPPAN), Alhaji Habibu Barde Mohammed, ya bayyana cewa auren zumunci ne aka ƙulla tsakanin ɗan sa Najib da sahibar sa A’isha a ranar Asabar.
Ya bayyana haka ne a hirar sa da mujallar Fim kan auren Najib Habibu Barde da abar ƙaunar sa A’isha Aminu Saley da aka ɗaura a safiyar shekaranjiya Asabar a gidan marigayi Malam Suley Ɗan Gogel da ke Layin Faruk Mustapha, daura da Layin Alhaji Sarauta, a Azare, Jihar Bauchi.
An yi walimar cin abinci a gidan mahaifin angon da ke GRA, Azare, bayan ɗaurin auren.


Haka kuma a ɓangaren gidan amarya, an yi walima ta mata a gidan mahaifin amarya, Alhaji Aminu Suley, wanda tsohon Mataimakin Shugaba (DCG) ne na Hukumar Kurkuku ta Nijeriya.
An kai amarya gidan ta bayan ango da abokan sa sun yi kilisa kan dawakai a yammacin ranar, wanda ya ƙayatar sosai.
Alhaji Habibu Barde Mohammed ya shaida wa mujallar Fim cewa auren haɗin gida aka yi, wato auren zumunci, domin kuwa mahaifin amaryar kawun shi mahaifin angon ne.
Wato dai an yi abin da Hausawa ke ce wa “dakan ɗaka shiƙar ɗaka”.

Haka kuma ya ce, “Mu na godiya ga dukkan waɗanda su ka halarci bikin tare da ɗaurin auren.
“Allah ya saka da alheri, ya bar zumunci, amin summa amin.
“Jiya Lahadi dukkan baƙi kowa ya koma gida lafiya lau. Mun gode wa Allah (s.w.t).”
Waɗanda su ka wakilci ‘yan Kannywood sun haɗa Alhaji Hamisu Iyan-Tama, Dakta Ahmed Sarari da Malam Nasiru Gwangwazo.
To, Allah ya ba Najib da A’isha zaman lafiya da zuri’a ɗayyiba, amin.


![]()






