‘Yan Kannywood da dama sun taya jaruma Radeeya Jibrin murna bayan ta ba da sanarwar bazata cewa ta yi aure.
Da alama, ta yi auren ne cikin sirri ba tare da sanar da kowa ba.
A yau Lahadi ne ta ba da sanarwar a shafin ta na Facebook.
A saƙon nata, ta bayyana tsananin yadda take son zaman aure a wannan lokacin ko don ‘ya’yan ta. Ta bayyana hakan ne bayan an sake ɗaura mata aure yau.
A cikin wani saƙon, jarumar ta ce: “Alhamdu lillah. Alhamdu lillah. Alhamdu lillah. Allah ka fi kowa sanin dalili na na son aure kuma na san duk wata jarabawa ta a kan aure kaine kake ɗora mini. Sannan kuma kai ne kake ƙara ƙaddara mini yin aure a lokacin da ka so. Allah na gode maka da wannan jarabawar taka a gare ni.
“Allah yadda na yi tawassali da kai, na yi imani da kai, na yarda da wannan auren domin ka domin gobe na domin yara na domin ‘yan’uwa na domin mahaifi na domin lahira ta.
“Allah ubangiji ka ba ni ikon ƙare rayuwa ta a ɗakin miji na. Allah Ubangiji ina roƙon ka don girman ka, don tsarkin ka don rahamar ka don darajar fiyayyen halitta Manzo sallallahu alaihi wasallam, Allah ubangiji ba don hali na ba, Allah yadda aka ɗaura mini aure yau, Allah Ubangiji ka sa sai dai a fitar da gawa ta a ɗakin miji na. Bissalam.”
Bayan ta wallafa sakon nata, ‘yan fim da ɗimbin masoyan ta sun taya ta murna da yi mata, tare da fatan Allah ya karɓi addu’ar ta kamar yadda ta rubuta cikin nuna neman yardar ta ga Ubangiji.
Jarumi Ali Nuhu ya taya ta murna tare da yi mata addu’ar Allah ya cika mata burin ta na zama a ɗakin mijin ta har ƙarshen rayuwar ta.
Shi ma Baballe Hayatu ya taya ta murna tare da yi mata fatan alheri.
Jaruma Saratu Abubakar kuma cewa ta yi: “Ba mu da abin da za mu ce sai Alhamdu lillah! In-sha Allah daga nan duniya till Janna, Radeeya Jibril. Congratulations once again.”
Shi ma jarumi Umar Gombe cewa ya yi: “Radeeya Jibril – Allah Ya ba ki zaman lafiya da zuri’a ɗayyiba. Amin.”

Furodusa Sani Arrahus shi ma ya bayyana a shafin kamfanin sa kamar haka: “Muna farin cikin sanar da auren Radeeya Jibril wadda aka ɗaura a yau Lahadi.
“Muna mata fatan alkhairi. Ubangiji Allah ya ba su zaman lafiya da zuri’a ɗayyiba albarkacin Manzon Allah sallallahu alaihi wasallam. Ubangiji Allah ka kau da dukkan sharri.”
![]()







