FITACCEN jarumi kuma darakta a Kannywood, Malam Al-Amin Ciroma, ya yi kira ga masu aibanta shi kan zaman auren sa da marigayiya Wasila Isma’il da su ji tsoron Allah su daina.
Ya ce idan har ba su tuba suka daina ba, to sai Allah ya tambaye su a ranar lahira. Mutane sun soki Ciroma da yin watsi da Wasila da ‘ya’yan su bayan mutuwar auren su.
Ciroma ya yi martani ga irin waɗannan mutanen ne a yau da Wasila ta cika kwana bakwai da rasuwa, cikin wani saƙo da ya wallafa a soshiyal midiya mai taken, “Addu’ar Bakwai na Wasila.”
Ga yadda cikakken rubutun nasa yake:
“ADDU’AR BAKWAI NA WASILA.
“A yau, Lahadi 31 ga Mayun 2026 ce rana ta bakwai bayan rasuwar UWAR ‘YA’YANA, WASILA ISMA’IL, wadda ta rasu a ranar 24 ga Mayu, 2026.
“A matsayi na na wanda ya zauna da ita, har na tsawon Shekaru 20, da watanni Takwas da kuma kwanaki 14, na tsaya kan kabarin ta, ina mai ƙara yi ma ta addu’a, tare da yafe ma ta kurakuran da duk ta yi mani, tun farkon zaman mu zuwa ranar da ta bar duniya.
“Saboda haka, zan yi amfani da wannan damar wajen nema mata yafiyar kowa daga cikin ‘yan’uwa da abokan arziki.
“Allah Ta’ala Ya gafarta ma Wasila, Ya sa ta huta. Mu kuma da ke raye, Allah Ta’ala Ya sa mu gama lafiya, bi Haqqi La’ila ha ilLah, Muhammadu Rasulullah (saw).
“A ƙarshe, ina yi mana NASIHA, musamman masu shiga sharo-ba-shanu, suke tura min saƙonni ko maganganu marasa daɗi, a yayin da ba su ma san me ya faru tsakanin mu da Wasila ba, DA SU JI TSORON ALLAH.
“Bai kamata kuna ta tsoma baki, kan abin da ba ku da ilimi a kai ba. Har masu wannan abin ba su Tuba sun daina ba, za su tsaya gaban Allah su bayar da shaida.
“Na yi ta samun saƙonni na private, da text messages ɗin da ba su da adadi kan rashin adalci da suke yi.
“A ƙarshe:
“Ni, Al-Amin Ciroma, fata na shi ne Allah Ya gafarta ma Wasila. Allah Ya gafarta wa iyayen mu, da dukkanin ‘yan’uwan mu da suka riga mu gidan gaskiya. Allah Ya sa sun huta.
“Mu kuma, Allah Ya sa mu gama lafiya, alfarmar Sayyidina Rasulullahi (sawa), Ameeeen 🤲
A. Ciroma
May 31, 2026.”
![]()







