• Gida
  • Labarai da Rahotanni
    • Labarai
    • Rahotonni
    • Tattaunawa
  • Sharhi da Tsokaci
    • Sharhin Fim
    • Tsokaci
  • Masu Haskawa
    • Taurarin Fim
    • Marubuta
    • Mawaƙa
  • Addini da Rayuwa
    • Rayuwa
    • Iyalai
    • Al’adu
    • Addini
  • Ranar Murna
Tuesday, August 25, 2026
  • Login
Kannywood - News, reviews and more  › hausa
  • Gida
  • Labarai da Rahotanni
    • Labarai
    • Rahotonni
    • Tattaunawa
  • Sharhi da Tsokaci
    • Sharhin Fim
    • Tsokaci
  • Masu Haskawa
    • Taurarin Fim
    • Marubuta
    • Mawaƙa
  • Addini da Rayuwa
    • Rayuwa
    • Iyalai
    • Al’adu
    • Addini
  • Ranar Murna
No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai da Rahotanni
    • Labarai
    • Rahotonni
    • Tattaunawa
  • Sharhi da Tsokaci
    • Sharhin Fim
    • Tsokaci
  • Masu Haskawa
    • Taurarin Fim
    • Marubuta
    • Mawaƙa
  • Addini da Rayuwa
    • Rayuwa
    • Iyalai
    • Al’adu
    • Addini
  • Ranar Murna
No Result
View All Result
Kannywood - News, reviews and more  › hausa
No Result
View All Result
  • Gida
  • Labari
  • Addini
  • Al’adu
  • Iyali
  • Marubuta
  • Mawaƙa
  • Nijeriya
  • Ranar Murna
  • Rayuwa
  • Sharhin Fim
  • Tattaunawa
  • Taurari
  • Tsokaci

Ƙungiyar ‘yan fim magoya bayan ta-zarcen Tinubu ta yi taron addu’ar neman zaman lafiya a Nijeriya

by MUKHTAR YAKUBU
June 22, 2026
in Labarai
0
Ƙungiyar ‘yan fim magoya bayan ta-zarcen Tinubu ta yi taron addu’ar neman zaman lafiya a Nijeriya

Makaranta Alƙur'ani a bakin aikin su a taron

0
SHARES
0
VIEWS
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsappShare on Telegram

ƘUNGIYAR ‘Yan Fim Masu Goyon Bayan Shugaban Ƙasa Bola Ahmed Tinubu domin ya sake yin wa’adi na biyu ta gudanar da taron addu’a da saukar Alƙur’ani mai tsarki domin neman zaman lafiya da kuma kawo ƙarshen matsalolin tsaro da suka addabi Nijeriya.

A taron da aka gudanar a yau Litinin a Filin Baje-koli da ke kan titin Gidan Zoo a cikin birnin Kano, membobin ƙungiyar daga sassa daban-daban na ƙasar nan tare da dattawan ƙungiyar sun halarta.

Da yake jawabi a wajen taron, Shugaban ƙungiyar na ƙasa, Alhaji Dauda Kahutu (Rarara), ya ce an shirya taron ne domin roƙon Allah ya kawo ƙarshen matsalolin tsaro da suka dabaibaye ƙasar nan.

Dauda Abdullahi Kahutu (Rarara) a wurin taron

Ya ce: “Mun shirya wannan taron addu’a ne domin mu roƙi Allah ya kawo mana ƙarshen matsalolin tsaro da ake fama da su a Nijeriya. Wannan matsala ta shafi kowa da kowa, musamman mu a Arewa, domin idan ba ta same ka kai-tsaye ba, za ta shafi wani na kusa da kai.”

Rarara ya ƙara da cewa matsalar tsaro ba ta gwamnati kaɗai ba ce, illa ta shafi dukkan al’umma, don haka wajibi ne kowa ya taka rawar da ta dace wajen nemo mafita.

“Harkar tsaro ba ta mutum ɗaya ba ce, ko shugaba ko talaka. Dole ne mu haɗa kai wajen samar da mafita ta hanyar addu’a da kuma taimaka wa hukumomin tsaro ta hanyar kai rahoton duk wani mutum ko motsi da ake zargi,” inji shi.

Dandazon mata a wurin taron

Ya kuma yi addu’ar Allah ya tona asirin duk masu hannu wajen haddasa matsalolin tsaro, ko suna cikin al’umma ko kuma a cikin gwamnati.

Bayan jawabin sa ne aka fara saukar Alƙur’ani, sannan aka ci gaba da gabatar da addu’o’i na neman zaman lafiya, tsaro da haɗin kan ƙasa.

A cikin addu’ar kammalawa, Malam Nura Hussaini ya yi addu’o’i masu tsawo, inda ya roƙi Allah ya kawo ƙarshen duk wani nau’in fitina da rashin tsaro da ake fama da shi a ƙasar nan.

Ya ce: “Ya Allah, Kana ganin halin da muke ciki na wahala da rashin tsaro. Muna roƙon Ka Ka kawo mana agaji, Ka hallaka masu tayar da fitina a duk inda suke. Duk wanda yake da hannu a wannan matsala, idan mai mulki ne Ka ƙwace mulkin sa, idan mai arziki ne Ka rage masa ikon da yake amfani da shi wajen cutar da jama’a.”

Mata a taron

Bayan kammala addu’ar, aka yanka sa da rago tare da raba sadaka ga mahalarta taron da sauran mabuƙata.

An gudanar da taron cikin lumana, inda aka fara shi lafiya kuma aka kammala shi lafiya.

Loading

Previous Post

Cewar Rahama Sadau: Rashin mahaifi na ya bar babban giɓi a rayuwa ta

Next Post

Kalaman Nafisa Abdullahi kan aure ba su wakilci kamfanin mu ba – Abnur Entertainment

Related Posts

Mutuwar aure na ƙaddara ce – Jaruma Khadija Yobe
Labarai

Mutuwar aure na ƙaddara ce – Jaruma Khadija Yobe

August 23, 2026
Aina’u Ade ta raba wa tsofaffin jaruman Kannywood tallafin kuɗi
Labarai

Aina’u Ade ta raba wa tsofaffin jaruman Kannywood tallafin kuɗi

August 23, 2026
Ƙungiyar ‘Triple R Kannywood’ ta ziyarci jarumi Tanimu Akawu a asibiti
Labarai

Ƙungiyar ‘Triple R Kannywood’ ta ziyarci jarumi Tanimu Akawu a asibiti

August 23, 2026
Ƙungiyar Triple R ta ba jarumin Kannywood Mustapha Musty tallafin N500,000
Labarai

Ƙungiyar Triple R ta ba jarumin Kannywood Mustapha Musty tallafin N500,000

August 18, 2026
Yadda na gamu da ibtila’in karaya a ƙafa – Jarumi Ɗan’azumi Kamaye
Labarai

Yadda na gamu da ibtila’in karaya a ƙafa – Jarumi Ɗan’azumi Kamaye

August 14, 2026
Tozali TV zai yi bikin Henna Ball da karrama masu ƙwazo da tallafa wa waɗanda suka tsira daga hare-hare a ranar 31 ga Oktoba
Labarai

Tozali TV zai yi bikin Henna Ball da karrama masu ƙwazo da tallafa wa waɗanda suka tsira daga hare-hare a ranar 31 ga Oktoba

August 8, 2026
Next Post
Kalaman Nafisa Abdullahi kan aure ba su wakilci kamfanin mu ba – Abnur Entertainment

Kalaman Nafisa Abdullahi kan aure ba su wakilci kamfanin mu ba – Abnur Entertainment

  • Home
  • Game Da Mu
  • Privacy Policy
  • Contact Us

© 2024 Mujallar Fim

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labari
  • Addini
  • Al’adu
  • Iyali
  • Marubuta
  • Mawaƙa
  • Nijeriya
  • Ranar Murna
  • Rayuwa
  • Sharhin Fim
  • Tattaunawa
  • Taurari
  • Tsokaci

© 2024 Mujallar Fim

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In
error: Content is protected !!