Gwamnatin Jihar Kano ta ba da umurnin rufe wani gini da ake zargin za a mayar da shi Dandalin Shirya Finafinai (film house) a Ɗorayi Ƙarama, cikin Unguwar Bello, a Ƙaramar Hukumar Gwale ta Jihar Kano.
Da yake zantawa da manema labarai jim kaɗan bayan rufe ginin, Shugaban Kwamitin Kar-ta-Kwana na Daƙile Gine-ginen da Ba Su Cika Ƙa’idoji ba, wanda kuma shi ne Shugaban Riƙo na Hukumar Tsara Birane ta Jihar Kano, Dakta Ɗalhatu Aliyu Sani, ya bayyana cewa ginin zai ci gaba da kasancewa a rufe har sai gwamnati ta kammala nazari kan lamarin.
Ya ce kwamitin zai ci gaba da bibiyar duk wani gini da aka dakatar da shi ko kuma ake gudanar da shi ba bisa ƙa’ida ba, domin ɗaukar matakin da ya dace.
An dai shafe kusan mako guda ana ta ce-ce-ku-ce kan wannan gini tun bayan da mamallakin sa, Sultan Abdurrazaq, ya bayyana aniyar sa ta buɗe Dandalin Shirya Finafinai a wurin nan gaba kaɗan.
Bayan sanarwar ne wasu mazauna unguwar Ɗorayi, waɗanda suka bayyana kan su a matsayin membobin kwamitin unguwa, suka rubuta takardar nuna rashin amincewa tare da miƙa ta ga hukumomin da abin ya shafa.
A ranar Talata, Shugaban Hukumar Tace Finafinai ta Jihar Kano, Alhaji Abba El-Mustapha, ya bayyana cewa lamarin ya isa gaban sa, inda ya gayyaci mamallakin wurin da kuma masu ƙorafi daga unguwar domin sasanta matsalar.
Sai dai, a cewar sa, har zuwa lokacin da aka tsara zaman, masu ƙorafin ba su halarta ba. Sultan Abdurrazaq ne kaɗai ya je tare da jiran zuwan su na wani lokaci, amma bayan ya ga sun ƙi bayyana, aka sallame shi ya tafi.
Daga baya ne masu ƙorafin suka isa ofishin, inda aka sanar da su cewa wanda suke ƙara ya riga ya tafi bayan ya jira su ba tare da sun zo ba. Daga nan aka nemi su sake dawowa a ranar Laraba domin ci gaba da tattaunawa.
Sai dai kafin a samu cikakken bayani kan sakamakon zaman da aka yi tsakanin ɓangarorin biyu a ranar Laraba, 24 ga Yuni, Hukumar Tsara Birane ta Jihar Kano ta ba da sanarwar rufe ginin tare da ɗaukar matakin dakatar da duk wani aiki a wurin.
Matakin da Hukumar Tsara Birane ta ɗauka kan wannan gini ya haifar da mabambantan ra’ayoyi a tsakanin al’umma, inda wasu suke ganin akwai yiwuwar siyasa ta shiga cikin lamarin.
Masu wannan ra’ayi na danganta hakan da kasancewar Sultan Abdurrazaq ɗan tafiyar Kwankwasiyya ne, kuma ya taɓa neman tikitin tsayawa takarar kujerar Majalisar Dokokin Jihar Kano a ƙarƙashin jam’iyyar NDP, amma bai samu nasarar samun tikitin ba.
Sai dai har zuwa lokacin haɗa wannan rahoto, hukumomin da abin ya shafa ba su yi wata sanarwa da ke nuna cewa matakin da aka ɗauka yana da alaƙa da siyasa ba.
![]()







