FITACCIYAR jaruma kuma furodusa a Kannywood, Hajiya Mansurah Isah ta fice daga ƙungiyar Triple R Kannywood for Renewed Hope, wadda ke goyon bayan Shugaba Bola Ahmed Tinubu, bayan wani saɓani da ya ɓarke tsakanin ta da shugabannin ƙungiyar.
Rahotannin da mujallar Fim ta samu sun nuna cewa saɓanin ya samo asali ne bayan wata tafiya da membobin ƙungiyar suka yi zuwa Abuja a kwanakin baya.
Majiyoyi sun bayyana cewa bayan kammala taron da suka halarta, Mansurah ta samu wata gayyata ta daban, inda aka buƙaci ta halarta tare da wasu daga cikin mutanen da ke tare da ita.
A cewar majiyoyin, jarumar ta nemi ta tafi da wasu daga cikin membobin da suka yi tafiyar Abuja tare da ita. Sai dai shugabannin ƙungiyar sun nuna rashin amincewa da hakan, suna mai cewa duk wata halarta ta irin wannan ya kamata ta kasance da sunan ƙungiyar Triple R Kannywood for Renewed Hope, ba da sunan mutum ɗaya ba.
Rahoton ya ce Mansurah ta nuna rashin gamsuwa da wannan matsaya, tana mai cewa ita ce aka gayyata kai-tsaye, don haka tana da damar zaɓar waɗanda za su raka ta.
Majiyoyin sun ce rashin daidaituwar fahimta kan wannan batu ne ya haifar da saɓanin da ya kai ga ficewar jarumar daga ƙungiyar.
Ƙungiyar Triple R Kannywood for Renewed Hope ta haɗa jaruman finafinai, mawaƙa, furodusoshi, daraktoci da sauran masu ruwa da tsaki a masana’antar Kannywood domin tallafa wa manufofin gwamnatin Shugaba Bola Ahmed Tinubu.
Alhaji Dauda Abdullahi Kahutu (Rarara) shi ne mai jagorantar ƙungiyar a matakin ƙasa, yayin da jarumi Lawan Ahmad yake riƙe da shugabancin reshen Kannywood.
Har zuwa lokacin haɗa wannan rahoto, babu wata sanarwa a rubuce daga Mansurah ko shugabannin ƙungiyar da ke tabbatar da ko musanta faruwar lamarin.
![]()







