GARIN Rimin Gado da ke Jihar Kano ya karɓi baƙuncin ɗimbin fitattun jaruman masana’antar Kannywood da suka hallara domin taya tsohuwar jaruma, Hajiya Halima Adam Yahaya, murnar auren ‘yar ta, Ummusalama Auwalu Maikano (Ummita).
An ɗaura auren ne a shekaranjiya Juma’a, 26 ga Yuni, a Babban Masallacin Juma’a da ke Rimin Gado da misalin ƙarfe 2:00 na rana, inda dangi, abokai da sauran al’umma suka taru domin shaida wannan muhimmin biki.
Bayan kammala ɗaurin auren, Halima ta shirya liyafa da misalin ƙarfe 3:00 na yamma domin murnar wannan rana.

Mahalartan bikin sun bayyana cewa wannan taro ya sake nuna kyakkyawar alaƙar da tsohuwar jarumar ta gina da abokan aikin ta tsawon shekarun da ta shafe a masana’antar.
Fitattun mahalartan sun haɗa da Zahara’u Shata, Fati Bararoji, Fati Sulaiman, Hauwa Waraka, Sadiya Gyale, Hajiya Zahara’u Adamar Kamaye, Bilkisu Madaki, Maijidda Ibrahim, Sakna Gadaz, Zakiyya Ibrahim, mawaƙi Salisu Mariri, marubuci kuma furodusa Zubairu Balannaji, marubuci Ayuba Muhammad Ɗanzaki, Rahama Sirace, da Hajiya Maryam Na’ibawa (Antima).

An gudanar da dukkan shirye-shiryen bikin cikin kwanciyar hankali da lumana.
Mahalarta sun yi addu’ar Allah ya albarkaci auren, ya ba su zaman lafiya, soyayya da zuri’a tagari.












![]()







