ALLAH ya yi, lokaci. Mawaƙi a Kannywood, Ahmad Usman Adamu, wanda aka fi sani da Ahmad Yariman Tiga, zai yi aure.
Za a ɗaura auren sa da sahibar sa, Maryam Bashir (Fulanin Yarima), a gobe Juma’a da misalin ƙarfe 1:00 na rana a Masallacin Muhammad Naseer da ke Kabala Road, Sabon Garin Tudun Wada, Kaduna.
Akwai walima da zarar an ɗaura auren.
Angon ya ce duk wanda bai samu damar halarta ba, ya yi masu addu’a.
Mujallar Fim ta ruwaito cewa Ahmad Yariman Tiga yana ɗaya daga cikin yaran shahararren mawaƙi Aminu Ladan Abubakar (ALA). Sai dai shi yana zaune ne a Kaduna.
![]()







