ƊIMBIN jama’a, ciki har da Gwamnan Jihar Kano, Alhaji Abba Kabir Yusuf, suka halarci jana’izar Hajiya Zainab Abdullahi Naniya, mahaifiyar jarumin Kannywood Isah A. Isah, wadda Allah ya yi wa rasuwa a ranar Litinin, 24 ga Nuwamba, 2025.
Kamar yadda mujallar Fim ta shaida maku a ranar, Hajiya ta rasu ne a wani asibiti da ke ƙasar Masar bayan ta yi kwana bakwai a asibitin.
Tun kafin a kai ta Masar ɗin dai, ta ɗauki lokaci tana kwance a asibiti a Kano inda daga baya aka fita da ita zuwa ƙasar wajen.
Hajiya Zainab Naniya, mai shekaru 62 a duniya, ita ce matar Farfesa Tijjani Naniya, mai ba Gwamnan Kano shawara a kan harkokin masarautun gargajiya.
Ta rasu ta bar ya’ya 8 – maza biyar, mata uku; Isah I. Isah ne babban ɗan ta.

An dawo da gawar Hajiya Zainab Nijeriya a jiya Alhamis, aka yi mata sallah da misalin ƙarfe 1 na rana a masallacin Juma’a na Khalifa Isyaka Rabi’u da ke Titin Malam Aminu Kano a cikin garin Kano.
Shugaban Majalisar Malamai ta Jihar Kano, Sheikh Ibrahim Khalil, shi ne ya jagoranci yi mata sallah, yayin da Gwamna Abba Kabir Yusuf da wasu daga cikin kwamishinonin sa da sauran manyan jami’an gwamnati suka halarta.
An rufe gawar Hajiya Zainab Naniya a maƙabartar bayan Gwauron Dutse, sannan aka ci gaba da zaman makoki a gidan mijin ta da ke kusa da gidan Khalifa Isyaka Rabi’u a Titin Malam Aminu Kano, inda dubun jama’a suke zuwa domin yin ta’aziyya.

‘Yan fim da dama sun shiga cikin dukkan mutanen da suke halarci jana’izar da kuma gidan gaisuwar. Daga cikin su akwai Alhaji Isma’ila Na’abba (Afakallah), Aminu A. Sharif (Momoh), Aminu Ilu Dambazau Auwalu Ɗangata, da sauran su.
Allah ya ji kan Hajiya Zainab, ya ba iyalai da ‘yan’uwan ta haƙurin jure wannan babban rashi, amin.


![]()







