ALLAH cikin ikon sa ya azurta mawaƙi kuma editan waƙoƙi Alhassan Abdulazeez (Babangida Afto) da ‘ya’ya mata ‘yan biyu, a shekaranjiya Alhamis, 6 ga Nuwamba, 2025.
Babangida da kan sa ya ba da sanarwar wannan ƙaruwar ta WhatsApp, inda ya ce, “Assalamu alaikum. ‘Yan’uwa da abokan arziki ina mai farin cikin sanar da ku cewa mai ɗaki na ta haifa mani tagwaye, duk mata.
“Muna buƙatar addu’ar ku, da fatan Allah ya ba mu ikon kula da su bisa koyarwar addinin Musulunci.”
Maiɗakin tasa, Malam Khadija Shu’aibu, ta haihu ne da misalin ƙarfe 2:55 na rana a asibitin gwamnati da ke Titin Kagoro, Kaduna.
An raɗa wa jariran suna Hassana da Hussaini.
A halin yanzu dai ‘ya’yan Babangida huɗu, dukkan su mata.
Mujallar Fim ta ruwaito cewa Babangida yaron fitaccen mawaƙi marigayi El-Mu’az Birniwa ne. Shi ke kula da ɓangaren situdiyo a kamfanin sa.
Allah ya raya su, ya kuma albarkaci rayuwar su.

![]()







