BAYAN fitaccen jarumin Kannywood Adam A. Zango ya bayyana cewa rabuwar sa da tsohuwar matar sa, jaruma Maimuna Musa, ta samo asali ne daga kasancewar dukkanin su masu Asperger Syndrome (A.S.), ita ma ta fito ta tabbatar da hakan.
A wani saƙo da ta wallafa a soshiyal midiya, Maimuna ta ce abin da tsohon mijin nata ya bayyana gaskiya ne, kuma wannan shi ne babban dalilin rabuwar su.
Ta ce: “Ni Maimuna Musa, tsohuwar matar Adam A. Zango, a yau ina so in tabbatar wa duk wanda ya ji ko ya san maganar da ya faɗa cewa, haƙiƙa, abin da ya ce gaskiya ne.
“Ya ce shi A.S. ne, ni ma A.S. ce, kuma wannan ne ya zama sanadin rabuwar mu. A yau ni ma na tabbatar da hakan. Wannan shi ne abin da ya faru, kuma na karɓi ƙaddarar Allah da zuciya ɗaya.”
Maimuna ta kuma bayyana cewa ba ta riƙe wani ƙorafi ko ƙiyayya a zuciyar ta ga tsohon mijin nata ba.
Ta ce tana yi masa fatan alheri tare da addu’ar Allah ya buɗe masa ƙofofin rahama da arziki, ya ba shi farin ciki na gaskiya, sannan ya haɗa shi da mace tagari wadda za ta zama alheri gare shi a duniya da lahira, tare da ba shi kwanciyar hankali da zaman lafiya.
Haka kuma, ta roƙi Allah ya zaɓa mata abin da ya fi alheri, tana mai cewa Shi ne mafi sanin abin da ya dace da bayin sa.
Ta kammala saƙon ta da addu’ar Allah ya ƙaddara alheri ga kowa.
A jiya ne mujallar Fim ta wallafa labarin rabuwar auren Zango da Maimuna, inda jarumin ya bayyana cewa bambancin halayen da ke tattare da kasancewar su dukkanin su masu A.S. ne ya sa suka yanke shawarar raba auren su cikin fahimtar juna.
Wataƙila fitowar Maimuna da ta tabbatar da bayanin Zango za ta kawo ƙarshen ce-ce-ku-cen da suka biyo bayan rabuwar auren, tare da nuna cewa sun rabu cikin mutuntawa da yi wa juna fatan alheri.
![]()







