BABBAN Hafsan Hafsoshin Sojan Nijeriya (COAS), Manjo-Janar Faruk Yahaya, ya bada agajin kuɗi naira miliyan biyu ga tsohon ɗan wasan kwaikwayo Alhaji Usman Baba Pategi (‘Samanja Mazan Fama), wanda ke fama da rashin lafiya.
Hukumar Dillancin Labarai ta Nijeriya (NAN) ta ruwaito cewa an kai wa Samanja tallafin ne a gidan sa da ke Kaduna a yau Litinin.
Rahoton hukumar, wanda mujallar Fim ta fassara, ya bayyana cewa wakilin Babban Hafsan askarawan, Birgediya-Janar Vitalis Okoro, wato Shugaban Ma’aikatan Kwamanda (GOC) na Runduna ta Ɗaya (1 Division) ta Sojojin Nijeriya da ke Kaduna, shi ne ya kai wa ɗan wasan wannan kuɗi har gida.
A jawabin da ya aika, Janar Yahaya ya bayyana cewa an sanar da shi halin rashin lafiya da Samanja ya ke ciki, wanda hakan ne ya sa ya ga ya kamata ya taimaka masa.
Ya ce rundunar Sojan Nijeriya na alfahari da kusanta kan ta da fitattun ‘yan ƙasa waɗanda su ka yi kyakkyawan tasiri ga al’umma.
A cewar sa, rundunar Sojan Nijeriya ta ji daɗin yadda Samanja ya riƙa inganta kyakkyawan zato game da rayuwar sojoji ga al’ummar Nijeriya ta hanyar wasan kwaikwayon sa, wanda hakan ya riƙa hasko yadda rayuwa ta ke a cikin barikokin soja.
Ya ce, “Ta hanyar wannan muhimmiyar rawar da ya taka, ya sama wa kan shi ɗaukaka a fagen harkokin nishaɗantarwa.

“Baya ga duk abin da Samanja ya yi na hasko kyakkyawan zato game da sojoji, ya kuma kasance abin so ga rundunar Sojan Nijeriya.”
Cikin farin ciki, Samanja ya maida jawabi inda ya tuno da aikin soja da ya taɓa yi.
Haka kuma ya ƙara ƙaryata ji-ta-ji-tar da aka yaɗa a kafafen soshiyal midiya a makon jiya cewa wai ya rasu.
Bugu da ƙari, Samanja ya bayyana matuƙar godiyar sa ga Babban Hafsan askarawan saboda wannan kulawa da ya nuna masa.
Daga nan ya yi kira ga dukkan ‘yan Nijeriya da su zama masu kishin ƙasa kuma su yi addu’ar ci gaba da samun zaman lafiya da juna a ƙasar nan.
Haka kuma ya yi kira ga matasa da a ko yaushe su kasance su na samu abin yi wanda zai amfani rayuwar su.
Ɗaya daga cikin ‘ya’yan Samanja, Amina Usman, ta bayyana cewa mahaifin ta mutum ne mai kula tare da ƙaunar iyalin sa.
Ita ma ta yi godiya ga rundunar Sojan Nijeriya saboda kulawar da ta yi wa iyalan Samanja.
Idan an tuna dai, a ranar Alhamis ta makon jiya an wayi gari da labarin wai Samanja ya kwanta dama.
Wani tsohon darakta a Hukumar Talbijin ta Ƙasa (NTA) ne ya yi kuskuren rubutawa a shafin sa na Facebook cewa Allah ya yi wa Samanja rasuwa.
Nan da nan labarin ya bazu a soshiyal midiya duk da yakefitaccen ɗan jaridar nan Ibrahim Sheme ya sanar da wanda ya yi rubutun da kuma jama’a cewa Samanja dai na nan da ran shi.
Sheme da ma’aikacin gidan talbijin ɗin nan na KSTV da ke Kaduna, wato Shafi’u Magaji Usman, su na aikin rubuta tarihin rayuwar Samanja, don haka sun san bai mutu ba.
Daga baya dai wanda ya fara bada labarin ya ɗauki gyara, kuma ya goge rubutun nasa tare da bada haƙuri.
Don ƙara dakushe yaɗuwar da labarin ‘rasuwar’ ke yi a soshiyal midiya, Shafi’u ya yi hirar bidiyo da Samanja a gidan sa da ke unguwar Kabala Costain a Kaduna, kuma aka yaɗa bidiyon, wanda hakan ya taimaka wajen daƙili labarin.
A hirar tasu, Alhaji Usman Baba Pategi ya bayyana cewa shi dai ya na nan da ran sa bai mutu ba.
Shi dai Alhaji Pategi, ya fara wasan kwaikwayo tun bayan dawowar sa daga Yaƙin Basasar Nijeriya, inda ya yi aikin soja, kuma ya ci gaba da gudanar da wasan ‘Samanja Mazan Fama’ da na ‘Duniya Budurwar Wawa’ a gidan Rediyon Tarayya na Kaduna har zuwa lokacin da ya yi ritaya saboda halin manyantaka da kuma rashin isasshiyar lafiya.
Mujallar Fim ta samu labarin yunƙurin da wasu ke yi a yanzu haka domin su yi masa ƙarin agaji saboda halin da ya ke ciki.


![]()








Masha Allah Allah ida nufi. #faroukyahaya #Babapategi #samanjamazanfama