• Gida
  • Labarai da Rahotanni
    • Labarai
    • Rahotonni
    • Tattaunawa
  • Sharhi da Tsokaci
    • Sharhin Fim
    • Tsokaci
  • Masu Haskawa
    • Taurarin Fim
    • Marubuta
    • Mawaƙa
  • Addini da Rayuwa
    • Rayuwa
    • Iyalai
    • Al’adu
    • Addini
  • Ranar Murna
Sunday, June 15, 2025
  • Login
Kannywood - News, reviews and more  › hausa
  • Gida
  • Labarai da Rahotanni
    • Labarai
    • Rahotonni
    • Tattaunawa
  • Sharhi da Tsokaci
    • Sharhin Fim
    • Tsokaci
  • Masu Haskawa
    • Taurarin Fim
    • Marubuta
    • Mawaƙa
  • Addini da Rayuwa
    • Rayuwa
    • Iyalai
    • Al’adu
    • Addini
  • Ranar Murna
No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai da Rahotanni
    • Labarai
    • Rahotonni
    • Tattaunawa
  • Sharhi da Tsokaci
    • Sharhin Fim
    • Tsokaci
  • Masu Haskawa
    • Taurarin Fim
    • Marubuta
    • Mawaƙa
  • Addini da Rayuwa
    • Rayuwa
    • Iyalai
    • Al’adu
    • Addini
  • Ranar Murna
No Result
View All Result
Kannywood - News, reviews and more  › hausa
No Result
View All Result
  • Gida
  • Labari
  • Addini
  • Al’adu
  • Iyali
  • Marubuta
  • Mawaƙa
  • Nijeriya
  • Ranar Murna
  • Rayuwa
  • Sharhin Fim
  • Tattaunawa
  • Taurari
  • Tsokaci

Addu’ar kwana 7: Zainab Booth ta ƙara samun kyakkyawar shaida

by DAGA MUHAMMAD LAWAN RANO
July 8, 2021
in Labarai
0
Addu’ar kwana 7: Zainab Booth ta ƙara samun kyakkyawar shaida
0
SHARES
0
VIEWS
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsappShare on Telegram

BAYAN kwana bakwai da rasuwar fitacciyar jaruma Zainab Booth, a yau Alhamis, 8 ga Yuli, 2021 ‘yan fim sun yi taron yi mata addu’a a Kano.

Ƙungiyar Matan Kannywood (Kannywood Women’s Association of Nigeria, K-WAN) ita ce ta shirya taron, wanda aka yi da misalin ƙarfe 4 na yamma a filin Social Welfare da ke unguwar Court Road. 

Taron, wanda ya samu halartar wasu daga cikin dattawa maza kuma malamai da ke masana’antar Kannywood domin jagorantar taron addu’ar.
 Malaman da su ka gabatar da addu’o’i na musamman a taron sun haɗa da Kabiru Nakwango, Hussaini Sule Ƙoƙi, Khalid Musa da Malam Inuwa. 

Da ya ke jawabi gabanin fara addu’o’in, Malam Inuwa ya yi nasihohi masu ratsa zukata inda ya bayyana cewa marigayiya Zainab mutuniyar kirki ce kuma mai ƙarfafa zumunci tsakanin ta da abokan sana’ar ta da sauran al’umma.

Ya ce: “Ba na mantawa, a duk lokacin da mu ka haɗu da wannan baiwar Allah sai ta tunasar da ni a kan cewa ta ba ni wasiyya da in yi mata addu’a tare da dangin ta da ma bayan rasuwar ta. Ba na mantawa da wannan abu; ga shi yau Allah ya karɓi rayuwar ta ta na mai samun kyakkyawan zato kamar yadda aka ji daga bakin mutane da dama.

“Ina jan hankalin ku da iyalan ta tare da sauran jama’a da su yi koyi da kyawawan ma’amalar ta tagari. 

Marigayiya Zainab Booth

“Mu yi amfani da damar da mu ke da ita wajen yin ayyukan da za su kai mu zuwa ga Aljanna. Wannan masana’anta idan mutum ya yi aikin daidai a cikin ta zai samu Aljanna, idan kuma aka samu akasin haka to fa sai dai addu’ar Allah ya kiyaye.”

A nasa bayanin, jarumi Malam Hussaini Sule Ƙoƙi ya maida hankali ne wajen tunasar da jaruman Kannywood da su bai wa batun addini muhimmanci domin kauce wa kallon da mutane su ke yi wa ‘yan masana’antar na yin burus da abubuwan da su ka shafi addini.

Shi kuma Kabiru Nakwango, ya yi bayani ne kan irin kyawawan halayen marigayiyar. Ya bayyana rashin Zainab Booth a matsayin wani babban rashi na jajirtacciyar mace.

Nakwango ya ce, “Hajiya Zainab na da kaffa-kaffa da duniya tare da gudun zuciya. Ba ta bari ko da wasa zargi ya ɗarsu a zuciyar wani, ba ma ita ba, duk yadda za ta yi sai ta yi domin ganin ta samar maka da farin ciki.  

“Zainab mai yawan addu’a ce tare da a duk lokacin da mu ka haɗu sai ta tambaye ni cewa ‘Ka na yi wa ‘ya’yan ka addu’a kuwa?’ 

“Wata rana ta kira ni, mu na karatu da ɗalibai, sai ta ji karatun yaran. Ta ce, ‘Na kira a kan gaɓa kenan?’ Sai kawai ta gaya min wata kalma guda ɗaya ta na sa ta a addu’a. Daga wannan magana, sai ta kashe wayar.

“Haƙiƙanin gaskiya, mun yi rashin mutuniyar kirki a cikin wannan masana’atar. Ya kamata a ce mata matasa su yi koyi da irin ɗabi’un ta da mutane su ke yabawa ko da yaushe. Mu bar bayan da za su yi mana addu’a tare da yin alfahari na alkairi wanda za mu gani, ba wai mu bar wa ‘ya’yan mu abin da za mu yi da-na-sani ba.”

Malam Kabiru Nakwango ya na jawabi

Jarumin ya kuma ja hankalin iyalan marigayiyar da su riƙe zumunci hannu biyu-biyu kamar yadda kowa ke shaidar Hajiya Zainab da shi.

Da ta ke jawabi a madadin shugabar ƙungiyar ta K-WAN, jami’a mai kula da tsare-tsaren ƙungiyar, Hajiya Rasheeda Adamu (Maisa’a) ta bayyana farin cikin da ta yi dangane da yadda ‘ya’yan wannan ƙungiya su ka amsa kiran yi wa marigayiyar addu’a.

Rasheeda ta ce, “Wannan shi ne karon farko da mu ka fara yin wannan taro na addu’a a tsakanin ‘yan wannan ƙungiya domin kuwa ita ce mace ta farko da ta fara komawa ga Mahaliccin ta tun bayan kafa ƙungiyar.”

Haka kuma ta bayyana cewa wannan taro ba zai zama na ƙarshe ba domin kuwa za su ci gaba da shirya addu’o’i da dama, ba wai sai dole an yi rasuwa ba. 

“Mu na addu’ar Allah ya gafarta wa Mama, ya yi mata Rahama.”

Da ya ke maida jawabi a madadin iyalan su, Shehu Abdullahi, babban ɗan Hajiya Zainab, ya bayyana farin ciki kan wannan taro da K-WAN ta shirya wa mahaifiyar su. 

Ya ce, “Wannan ya nuna yadda mahaifiyar mu ta yi zama da mutane lafiya da ƙaunar juna. Ba mu da abin da za mu ce sai dai Allah ya yi mata rahama, ya kuma saka wa kowa da alkairi.”

A ƙarshe, ya buƙaci jama’ar da ke wannan masana’anta da cewa duk wanda su ka san su na bin mahaifiyar tasu bashi ko ta ke bi da su taimaka su yi magana domin a sauke mata nauyi.

Taron addu’ar ya samu halartar Kwamishinar Harkokin Mata ta Jihar Kano, Dakta Zahra’u Muhammad, wadda ta yi nasiha ga mata da su kula da irin suturar da za su saka wanda ya dace tare da guje wa abubuwan da su ka san sun saɓa wa addini da al’adar mu.

Dandazon mahalarta

Ɗimbin dattawa da matan Kannywood da kuma ‘yan’uwan marigayiyar da su ka zo daga sassan ƙasar nan da dama sun halarci taron.

Cikin jaruman da mujallar Fim ta gani akwai Maryam Dodo, Fati Bararoji, Maryam CTV, Safiya Kishiya, Fati Al-Amin, Jamila Nagudu, Teema Yola, Hadiza Kabara, Hauwa Waraka, Siddiqa Jibril, Aina’u Ade, Hajara Usman, Momee Gombe, Rasheeda Maisa’a, Sadiya Shehu da Batula Hussain.

Mazan kuwa sun haɗa da Kabiru Maikaba, Malam Inuwa, Ahmad Alkanawy, Yusuf Haruna Funtuwa (Baban Chinedu), Rabi’u Lawan, Hussaini Ali Ƙoƙi, Baballe Hayatu, Yakubu Furodusa da sauran su.

An gudanar da taron tare da ɗaukacin ‘ya’yan marigayiyar su huɗu, wato Shehu, Sadiya, Maryam da kuma Ahmad (Amude).

Allah ya jiƙan Hajiya Zainab Booth, amin

Malam Khalid da Malam Inuwa su na gabatar da jawabi
Kwamishinar Al’amuran Mata, Dakta Zara’u Muhammad, a wajen taron
Rasheeda Adamu Maisa’a (a hagu) tare da Kwamishinar Al’amuran Mata, Dakta Zara’u Muhammad (a tsakiya) da wata bayan an kammala taron

Loading

Tags: Dakta Zahra'u MuhammadKabiru NakwangoKannywoodMaryam BoothRasheeda Adamu Maisa'aZainab Musa Booth
Previous Post

Yadda shirin N-Power ke zaburar da miliyoyin matasa taka tudun dogaro da kai

Next Post

Hoto: Alhinin Amude Booth a gaban kabarin mamar shi

Related Posts

Wani maigida na ya ce wahalar banza nake yi a kan Yerima Shettima, inji Hussaini Danko
Labarai

Wani maigida na ya ce wahalar banza nake yi a kan Yerima Shettima, inji Hussaini Danko

June 13, 2025
Jarumin Kannywood, Abdul M. Shareef zai auri jaruma Maryam Malika
Labarai

Jarumin Kannywood, Abdul M. Shareef zai auri jaruma Maryam Malika

June 12, 2025
Hukumar Tace Finafinai ta Kano ta yaba wa ɗakunan taruka bisa bin doka da oda lokacin bukukuwan Sallah
Labarai

Hukumar Tace Finafinai ta Kano ta yaba wa ɗakunan taruka bisa bin doka da oda lokacin bukukuwan Sallah

June 12, 2025
Rahama Sadau ta raba barka da Sallah ga ‘yan fim na Kaduna
Labarai

Rahama Sadau ta raba barka da Sallah ga ‘yan fim na Kaduna

June 11, 2025
‘Aure tsakanin jaruman Kannywood, Mansurah da Momoh’: Yadda lamarin yake
Labarai

‘Aure tsakanin jaruman Kannywood, Mansurah da Momoh’: Yadda lamarin yake

June 11, 2025
An naɗa Shehu Hassan Kano shugaban riƙo na MOPPAN
Labarai

An naɗa Shehu Hassan Kano shugaban riƙo na MOPPAN

June 3, 2025
Next Post
Hoto: Alhinin Amude Booth a gaban kabarin mamar shi

Hoto: Alhinin Amude Booth a gaban kabarin mamar shi

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

  • Home
  • Game Da Mu
  • Privacy Policy
  • Contact Us

© 2024 Mujallar Fim

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labari
  • Addini
  • Al’adu
  • Iyali
  • Marubuta
  • Mawaƙa
  • Nijeriya
  • Ranar Murna
  • Rayuwa
  • Sharhin Fim
  • Tattaunawa
  • Taurari
  • Tsokaci

© 2024 Mujallar Fim

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In
error: Content is protected !!