• Gida
  • Labarai da Rahotanni
    • Labarai
    • Rahotonni
    • Tattaunawa
  • Sharhi da Tsokaci
    • Sharhin Fim
    • Tsokaci
  • Masu Haskawa
    • Taurarin Fim
    • Marubuta
    • Mawaƙa
  • Addini da Rayuwa
    • Rayuwa
    • Iyalai
    • Al’adu
    • Addini
  • Ranar Murna
Sunday, June 15, 2025
  • Login
Kannywood - News, reviews and more  › hausa
  • Gida
  • Labarai da Rahotanni
    • Labarai
    • Rahotonni
    • Tattaunawa
  • Sharhi da Tsokaci
    • Sharhin Fim
    • Tsokaci
  • Masu Haskawa
    • Taurarin Fim
    • Marubuta
    • Mawaƙa
  • Addini da Rayuwa
    • Rayuwa
    • Iyalai
    • Al’adu
    • Addini
  • Ranar Murna
No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai da Rahotanni
    • Labarai
    • Rahotonni
    • Tattaunawa
  • Sharhi da Tsokaci
    • Sharhin Fim
    • Tsokaci
  • Masu Haskawa
    • Taurarin Fim
    • Marubuta
    • Mawaƙa
  • Addini da Rayuwa
    • Rayuwa
    • Iyalai
    • Al’adu
    • Addini
  • Ranar Murna
No Result
View All Result
Kannywood - News, reviews and more  › hausa
No Result
View All Result
  • Gida
  • Labari
  • Addini
  • Al’adu
  • Iyali
  • Marubuta
  • Mawaƙa
  • Nijeriya
  • Ranar Murna
  • Rayuwa
  • Sharhin Fim
  • Tattaunawa
  • Taurari
  • Tsokaci

Aishatu Musa Dalil, ‘yar shekara 18, ta lashe gasar rubutu ta ‘Hikayata’ ta 2021

by DAGA IRO MAMMAN
November 26, 2021
in Marubuta
1
Aishatu Musa Dalil, gwarzuwar gasar 'Hikayata' ta bana, riƙe da kambin ta a zaure taron karramawar

Aishatu Musa Dalil, gwarzuwar gasar 'Hikayata' ta bana, riƙe da kambin ta a zaure taron karramawar

0
SHARES
0
VIEWS
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsappShare on Telegram

AISHATU Musa Dalil ta lashe gasar rubutun gajerun labaran ƙirƙira ta ‘Hikayata’ ta bana.

An bayyana haka ne a wani ƙwarya-ƙwaryan shagali wanda aka shirya a daren yau a ɗakin taro na Ladi Kwali da ke otal ɗin Sheraton da ke Abuja.

Gidan rediyon BBC Hausa ne ke shirya gasar a kowace shekara.

Aisha, wadda ke zaune a Kaduna amma ‘yar asalin Jihar Adamawa ce, ‘yar shekara 18, wanda hakan ya sa ta kasance marubuciya mafi ƙarancin shekaru tun da aka fara gasar shekaru shida da su ka gabata.

Ta zama zakara ne da gajeren labarin ta mai suna ‘Haƙƙi Na’, wanda jigon sa shi ne fyaɗe.

Nana Aicha Hamissou Abdoulaye, ‘yar shekara 27 da ta zo daga Maraɗi a Jamhuriyar Nijar, ta zo ta biyu da gajeren labarin ta mai suna ‘Butulci’. 

Zauren taro na Ladi Kwali da ke cikin otal ɗin Sheraton inda aka yi bikin karramawar

Zulaihat Alhassan, ‘yar shekara 29 da ta zo daga garin Kaduna amma ‘yar asalin Jihar Kebbi ce, ita ce ta zo ta uku da labarin ta mai taken ‘Rahmat’.

An ba gwarzuwar gasar kyautar tsabar kuɗi dalar Amurka dubu biyu ($2,000) da lambar yabo; an ba ta biyu dala dubu ɗaya ($1,000) da lambar yabo, sannan an ba ta uku dala ɗari biyar ($500) da lambar yabo.

Wannan shi ne karo na farko da wata marubuciya daga ƙasar waje ta samu nasara a gasar.

Taron ya samu halartar manyan baƙi da su ka haɗa da Gwamnan Jihar Jigawa, Alhaji Badaru Abubakar, da uwargidan Gwamnan Jihar Kano, Dakta Hafsat Abdullahi Umar Ganduje (Goggo), da tsohon sanata Comrade Shehu Sani.

Akwai kuma ‘yan siyasa, ‘yan kasuwa, ma’aikatan gwamnati, ‘yan jarida, marubuta, da sauran jama’a daga sassa daban-daban na rayuwa.

Mutane da dama sun yi jawabi, ciki har da na shugabar alƙalan gasar a bana, Dakta Hauwa Bugaje ta Jami’ar Ahmadu Bello, Zariya, wadda ta bayyana tasirin rubutu a cikin al’umma da yadda aka samar da zakarun gasar ta bana.

Shi kuma shugaban Sashen Hausa na BBC, Malam Aliyu Abubakar Tanko, ya yi jawabin maraba tare da bayyana sadaukarwar da BBC Hausa ke da ita wajen amfani da soshiyal midiya don ƙara kusantar jama’a.

Zauren taron

A jawabin, ya sanar da jama’a cewa nan gaba kaɗan BBC Hausa za ta buɗe shafi a manhajar nan ta TikTok a ƙoƙarin ta na faɗaɗa ayyukan ta a kafofin sada zumunta na zamani.

Haka kuma ya bayyana cewa shirye-shirye sun kankama wajen tsara gagarumin bikin cikar BBC Hausa shekaru 65 da kafuwa, har ya bada tabbacin cewa Shugaban Ƙasa Muhammadu Buhari ma zai halarta.

A nasa jawabin, Gwamna Badaru ya bayyana farin ciki kan yadda BBC ke shirya wannan gasa, ya ce hakan zai taimaka wajen bunƙasa harshen Hausa.

Ya yi la’akari da cewa tunda an ce alƙalami ya fi takobi kaifi, abin da BBC ke yi zai taimaka gaya wajen isar da saƙonnin Hausa ga sassan duniya.

Haka kuma ya ɗau alƙawarin cewa zai taimaka wa zakarun gasar ta bana su samu aiki da zaran sun kammala karatun su.

Ya ƙara da cewa shi da uwargidan gwamnan Kano za su haɗa kuɗi domin a ƙara wa zakarun gasar kyautar da BBC ta yi masu.

Ita kuma Dakta Hafsat Ganduje, ta gode wa Allah kan ayyukan da BBC Hausa ke yi.

Ta yi murna da ganin cewa Aicha daga Nijar ta samu wannan kyauta da kuma yadda ‘yan wasu ƙasashen su ka shiga gasar domin hakan shaida ce mai nuna faɗaɗar harshen Hausa a duniya.

Dakta Hafsat ta yi fatan cin wannan gasa zai kasance buɗin basira ga zakarun gasar.

Ta ce a shirye ta ke ta taimaka wa wannan tsari na haɓaka harshen Hausa.

Masu jawabai sun haɗa da Darakta-Janar na Hukumar Kula da Gidajen Rediyo da Talbijin ta Ƙasa (NBC), Alhaji Balarabe Shehu Illela, da takwaran sa na Hukumar Gidajen Rediyon Tarayya (FRCN), Dakta Mansur Liman, waɗanda dukkan su ma’aikatan BBC ne a da.

Yayin da Balarabe ya riƙa aiko wa BBC da rahotanni daga birnin Beijing na ƙasar Chaina, shi kuma Mansur ya taɓa shugabantar Sashen Hausa na BBC.

Su kuma zakarun gasar, an ba Aisha Musa Dalil dama ta ce wani abu a madadin su, inda ta yi godiya ga Allah da Gwamna Badaru da kuma ma’aikatan BBC Hausa saboda wannan karramawa da su ka samu.

Sai dai mujallar Fim ta lura da cewa a ƙarshe Aisha ta kasa ci gaba da magana saboda kukan murna da ya sarƙe ta.

Wani abu wanda ya ƙara ƙayatar da taron shi ne  nishaɗantar da mahalarta da fitacciyar mawaƙiyar nan da ke tashe, Khairat Abdullahi, ta yi da waƙoƙin ta, ciki har da wata waƙa da ta yi wa BBC Hausa.

Gwamna Badaru Abubakar Ɓaɓura ya na miƙa wa Aisha Musa Dalil kambin wadda ta zo ta ɗaya

A ƙarshen taron, Haruna Shehu Tangaza na BBC ya yi jawabin godiya, sannan aka bada dama ga jama’a da su ɗebi abinci da abin sha da aka shirya da kan su.

Daga nan an ci gaba da ɗaukar hotuna da yin musabaha da juna har zuwa lokacin da aka fara watsewa.

Malam Ibrahim Isa ne ya yi aikin mai gabatarwa a taron, kuma an riƙa yaɗa yadda taron ke gudana kai-tsaye ga masu kallo a shafin BBC Hausa na Facebook.

Yanzu dai gwarzayen gasar ‘Hikayata’ na shekaru shida su ne kamar haka:

2021 – Aishatu Musa Dalil

2020 – Maryam Umar

2019 – Safiyya Ahmad

2018 – Safiyya Jibril Abubakar

2017 – Maimuna Sani Idris Beli

2016 – A’isha Mohammed Sabitu

An tashi daga taron na daren yau da misalin ƙarfe 10.

Dakta Hafsat Ganduje ta na miƙa wa Aicha Hamissou Abdoulaye kambin wadda ta zo ta biyu
Zulaihat Alhassan ta karɓi kambin wadda ta zo ta uku daga hannun Malam Sadiq Mai Borno, Mataimakin Manajan Darakta na NLNG
Gwarzayen gasar jim kaɗan bayan sun karɓi kyaututtukan su
Aisha Musa Dalil na gabatar da jawabin godiya a madadin sauran gwarzayen
Gwarzayen gasar sun yi hoto da manyan baƙi
Fitacciyar zabiya Khairat Abdullahi ta na nishaɗantar da taron da waƙoƙin ta
Edita kuma shugaban Sashen Hausa na BBC, Aliyu Abubakar Tanko, ya na gabatar da jawabin sa
Uwargidan Gwamnan Kano, Daga Hafsat Ganduje (Gwaggo), ta na gabatar da jawabin ta
Teburin manyan baƙi
Gwarzayen gasar a wajen bikin
Mai gabatarwa, Ibrahim Isa, a bakin aikin sa
Ibrahim Sheme da Hajiya Hafsat Abdulwaheed a wurin taron.

Loading

Tags: Aishatu Musa DalilAliyu TankoBalarabe Shehu IllelaBBC HausaComrade Shehu SaniDakta Hafsat GandujeDakta Mansur LimanDr Hauwa BugajeGwamna Badaru AbubakarHikayataKhairat AbdullahiNana Aicha Hamissou AbdoulayeZulaihat Alhassan
Previous Post

Za a ƙaddamar da sabon bugu na littafin tarihin Daular Usmaniyya a ranar Talata

Next Post

Gobe za a zaɓi sabbin shugabannin MOPPAN na Kaduna

Related Posts

Gasar rubutu: Ba a taɓa ba marubutan Hausa dama irin wannan ba – Balannaji 
Marubuta

Gasar rubutu: Ba a taɓa ba marubutan Hausa dama irin wannan ba – Balannaji 

January 1, 2025
Zubairu Balannaji ya zama gwarzon gasar rubutu ta Hukumar Tace Finafinai
Marubuta

Zubairu Balannaji ya zama gwarzon gasar rubutu ta Hukumar Tace Finafinai

December 31, 2024
‘Dakan ɗaka…’: Kanawa sun lashe gasar rubutu ta Hukumar Tace Finafinai
Marubuta

‘Dakan ɗaka…’: Kanawa sun lashe gasar rubutu ta Hukumar Tace Finafinai

December 20, 2024
Mutane 15 sun yi nasarar zuwa zagayen kusa da na ƙarshe a gasar rubutu na Hukumar Tace Finafinai
Marubuta

Mutane 15 sun yi nasarar zuwa zagayen kusa da na ƙarshe a gasar rubutu na Hukumar Tace Finafinai

November 30, 2024
Tsakanin matan aure biyu da budurwa ɗaya za a san gwarzuwar gasar Hikayata ta 2024 a yau
Marubuta

Tsakanin matan aure biyu da budurwa ɗaya za a san gwarzuwar gasar Hikayata ta 2024 a yau

November 27, 2024
Ƙungiyar matasa da mata za ta naɗa Ado Gidan Dabino Sarkin Mawallafan Arewa
Marubuta

Gasar rubutu: Hukumar Tace Finafinai ta bayyana gwaraza 50 na zagayen farko

November 24, 2024
Next Post
Hajiya Fatima Lamaj da Alhaji Hamisu Jibrin Goma, 'yan takarar shugabancin MOPPAN a Kaduna

Gobe za a zaɓi sabbin shugabannin MOPPAN na Kaduna

Comments 1

  1. Jamila Adamu Yaro says:
    4 years ago

    Masha Allah ina taya su murna Allah qara jagora amin

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

  • Home
  • Game Da Mu
  • Privacy Policy
  • Contact Us

© 2024 Mujallar Fim

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labari
  • Addini
  • Al’adu
  • Iyali
  • Marubuta
  • Mawaƙa
  • Nijeriya
  • Ranar Murna
  • Rayuwa
  • Sharhin Fim
  • Tattaunawa
  • Taurari
  • Tsokaci

© 2024 Mujallar Fim

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In
error: Content is protected !!