FITACCIYAR jarumar Kannywood, Fatima S.U. Garba, ta bayyana cewa akwai wasu abubuwa gudu uku waɗanda ba za ta taɓa mantawa game da mahaifiyar ta ba, wadda Allah ya yi wa rasuwa a shekaranjiya Asabar, 18 ga Satumba, 2021.
Hajiya Hauwa S.U. Garba ta rasu ne da misalin ƙarfe 6:00 na safe a wani asibiti mai suna Adede Specialist Hospital da ke Minna, Jihar Neja, bayan ta yi doguwar jinya.
Ta rasu ta na da shekara 64 a duniya, kuma ta bar ‘ya’ya.
A yayin da ta ke yi wa mujallar Fim ƙarin bayani game da wannan babban rashi na mahaifiyar ta, jarumar wadda aka fi sanu da Fati S.U., ta lissafa manyan abubuwa uku da ba za ta taɓa mantawa da su ba game da Hajiya.
Su ne: kawo ta duniya da ta yi, tarbiyyar da ta yi mata wadda ta sa ta na ɗaya daga cikin jarumai mata masu kamun kai a masana’antar finafinan Hausa, da kuma albarkar da ta sanya wa ‘ya’yan ta a gab da lokacin da za ta rasu.
Jarumar ta ce: “Iyaye su na da muhimmanci a rayuwar ‘ya’yan su gaba ɗaya, amma ba ni da wani a rayuwa ta da ya fi min muhimmaci kamar mahaifiya ta saboda ta zama jigon rayuwa gaba ɗaya.
“Duk da cewa Allah ne ya ke da mutum, amma tarbiyyar da ta yi mani ai ta yi ƙoƙari. A Kannywood ba zan zama ta ɗaya ko ta biyu ba a masu kamun kai, alhamdu lillahi dai.
“Sannan abin da ba zan taɓa mantawa da shi ba wanda ta yi min shi ne kawo ni duniya da ta yi; wannan ba zan taɓa mantawa da shi ba.
“Kuma kafin ta cika sai da ta sa wa duk ‘ya’yan ta albarka, kuma ta ce mana Allah ya sa mu gama da duniya lafiya.”
Ɗimbin ‘yan fim sun taya Fati alhinin wannan rashi da ta yi, kuma sun yi addu’ar Allah ya jiƙan Hajiya.
Fati ta faɗa wa wakilin mu cewa wasu daga cikin ‘yan fim sun je sun yi mata ta’aziyya, amma ba sai ta faɗi sunan su ba, sannan wasu kuma su na kan hanyar zuwa.
To, Allah ya jiƙan Hajiya Hauwa, ya albarkaci abin da ta bari, amin.
![]()








Allah ya jikanta yayi mata rahama ya gafarta mata
Allah ya baiwa “Yan uwanta hankurin jure rashinta amin